Home General NFIU ta magantu kan dokar haramtawa Gwamnoni cirar kudi a Asusun...

NFIU ta magantu kan dokar haramtawa Gwamnoni cirar kudi a Asusun Gwamnati

Hukumar tattara bayanan sirri kan harkokin kuɗi ta Najeriya ”Nigerian Financial Intelligence Unit” (NFIU) ta ce haramcin da take ƙoƙarin sanyawa kan cire kuɗi daga asusun gwamnatin tarayya da na jihohi abu ne da zai taimaka wa gwamnonin ba cutar da su ba.

Hukumar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar ta hannun jami’inta na hulda da jama’a Ahmed Dikko sa’o’i bayan ƙungiyar gwamnonin ƙasar ta soki sanarwa da hukumar ta fitar ranar 5 ga watan Janairu, ta umartar bankuna da su dakatar da bai wa gwamnoni kudaɗe daga asusun gwamnati daga ranar 1 ga watan Maris mai zuwa.

“Sabuwar dokar da hukumar NFIU ke shirin ƙaƙabawa game da sha’anin shige da ficen kuɗi baya cikin tsarin dokokin da ayyukan hukumar” Kamar yadda ƙungiyar gwamnonin ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar.

Ƙungiyar gwamnonin ta kuma kafa kwamiti mai mambobi shida da za su tattauna da babban bankin ƙasar domin duba batun matsalolin sha’anin harkokin kuɗi da ƙasar ke fuskanta.

A martanin da hukumar ta NFIU ta fitar ta ce a shirye take domin hada kai da kwamitin da ƙungiyar gwamnonin ta kafa domin wayar musu da kai game muhimmancin sabon kuɗurin.

”Sannan abun da muke ƙoƙarin aiwatarwa bai saɓa doka ba. Mun bayar da ƙa’idar ne domin magance tarin bincike da muka hango wa gwamnonin. Mun sanya ƙa’idar ce domin taimaka wa gwamnonin ba don cutar da su ko wani ma’aikacin gwamnati ba” kamar yadda sanarwar da NFIU ta fitar.

Sannan kuma hukumar ta ce a baya ta sanya makamanciyar wannan doka kan ƙananan hukumomi, inda aka kai ta kotu, amma kuma sai ta yi nasara a kotun.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu MohammedJami'an Tsaro Sun Kai Farmaki Sansanin IPOB/ESN, Sun Kawar da 'Yan Ta'adda 6 a AnambraOperation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Lalata Motocin Yaƙi Guda Biyu na ISWAP, Sannan Ya Kawar da Ƴan Ta'adda da Dama a BornoMai fafutuka Mahdi Shehu ya yi Gargadin Cewa Kudirin Dokar NGO Zai iya Shafar Masallatai, Coci, da Ƙungiyoyin ɗalibaiRikicin Karkashin Mulkin APC a Katsina: ADC na Radda da CSO Har Yanzu Suna Tsare a Hannun Masu ba Tinubu Shawara, MasariAnambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.
X whatsapp