Home General Majalisar wakilai tace za’a kamu Mata Emefiele

Majalisar wakilai tace za’a kamu Mata Emefiele

Shugaban Majalisar Wakilan, Femi Gbajabiamila ya bayyana fushinsa kan yadda gwamnan babban bankin ya ki halartar zama tare da wani kwamitin wucen-gadi na majalisar karkashin jagorancin Alhassan Ado Doguwa.

A cikin wata wasika da Emefiele ya aike wa zauren majalisar a wannan Alhamis ya bayyana cewa, ba zai samu damar halartar zaman ba.

Majalisar Wakilan ta gayyace shi domin yi mata bayani game da gazawar bankin na CBN wajen wadata sassan Najeriya da sabbin takarddun kudin Naira a daidai lokacin da wa’adin ranar 31 ga watan nan na Janairiu na daina amfani da tsoffin kudin ya kusan cika.

.

Da dama daga cikin ‘yan Najeriya na farbagar halin da za su tsinci kansu a ciki muddin wa’adin daina amfani da tsoffin Naira ya kawo karshe ba tare da sauya musu da sabbin ba, lamarin da masana tattalin arziki ke cewa, zai jefa miliyoyin mutanen kasar cikin talauci.

Gwamnatin tarayya ta ce, ba za ta tsawaita wa’adin ba kamar yadda ‘yan kasar suka bukata, yayin da ‘yan kasuwa ke kokawa kan rashin musanya musu tsohuwar Nairar da sabuwa a bankunan kasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp