Home General Amurka ta bayyana Nijeriya matsayin kasa mai muhimmanci ga duniya

Amurka ta bayyana Nijeriya matsayin kasa mai muhimmanci ga duniya

Amurka ta bayyana Nijeriya matsayin kasa mai muhimmanci ga duniya baki daya, ga da bukatar yan kasar su gudanar da zabe cikin lumana.

Wannan na Wani sako na musamman da manyan jami’an gwamnatin kasar suka nada ta bidiyo mai tsawon mintina 58 suka kuma aikewa jama’ar kasar,

Sakon da ya janyo hankalin ‘yan siyasa da kuma jama’a baki daya da su bada gudumawa wajen ganin anyi zabe mai inganci a karshen wannan mako.

Cikin wadanda suka gabatar da sakonninsu a bidiyon sun hada da Sakataren harkokin waje Anthony Blinken da Babbar jami’ar USAID Samantha Power da Jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya Linda Thomas-Greenfield.

Sakon ya bayyana cewar ‘yan Najeriya sun sake samun wata dama na bayyana ra’ayoyinsu da kuma zabin shugaban da suke bukata ta hanyar zabe saboda muhimmancin kuri’un su.

Blinken yace muhimmancin wannan zaben da zai gudana a karshen wannan mako ba wai ya tsaya kawai ga Najeriya bane, har ma da duniya baki daya.

Wakilan gwamnatin sun jaddada cewar Amurka bata goyan bayan wani ‘dan takara guda, amma kuma tana goyan bayan shirin wanda zai baiwa jama’ar kasar zabin abinda suke so ta hanyar lumana.

Sakon yace samun gudanar da karbabben zaben cikin kwanciyar hankali zai taimaka wajen samun dorewar zaman lafiya a duniya baki daya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp