Home General Amurka ta bayyana Nijeriya matsayin kasa mai muhimmanci ga duniya

Amurka ta bayyana Nijeriya matsayin kasa mai muhimmanci ga duniya

Amurka ta bayyana Nijeriya matsayin kasa mai muhimmanci ga duniya baki daya, ga da bukatar yan kasar su gudanar da zabe cikin lumana.

Wannan na Wani sako na musamman da manyan jami’an gwamnatin kasar suka nada ta bidiyo mai tsawon mintina 58 suka kuma aikewa jama’ar kasar,

Sakon da ya janyo hankalin ‘yan siyasa da kuma jama’a baki daya da su bada gudumawa wajen ganin anyi zabe mai inganci a karshen wannan mako.

Cikin wadanda suka gabatar da sakonninsu a bidiyon sun hada da Sakataren harkokin waje Anthony Blinken da Babbar jami’ar USAID Samantha Power da Jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya Linda Thomas-Greenfield.

Sakon ya bayyana cewar ‘yan Najeriya sun sake samun wata dama na bayyana ra’ayoyinsu da kuma zabin shugaban da suke bukata ta hanyar zabe saboda muhimmancin kuri’un su.

Blinken yace muhimmancin wannan zaben da zai gudana a karshen wannan mako ba wai ya tsaya kawai ga Najeriya bane, har ma da duniya baki daya.

Wakilan gwamnatin sun jaddada cewar Amurka bata goyan bayan wani ‘dan takara guda, amma kuma tana goyan bayan shirin wanda zai baiwa jama’ar kasar zabin abinda suke so ta hanyar lumana.

Sakon yace samun gudanar da karbabben zaben cikin kwanciyar hankali zai taimaka wajen samun dorewar zaman lafiya a duniya baki daya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp