Home General Gwamnatin Tarayyar Nijeriya tayi Martani kan Bukatar Obasanjo

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya tayi Martani kan Bukatar Obasanjo

Gwamnatin Najeriya ta ce tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ba shi da “wata kimar” da zai nemi a dakatar da tattara sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da ake yi yanzu haka a ƙasar.

Gwamnatin ta mayar masa da martani ne bayan wasiƙar da ya rubuta a yammacin Litinin, yana mai neman Shugaba Muhammadu Buhari da shugaban hukumar zaɓe Mahmood Yakubu su soke sakamakon wasu yankuna da ya yi zargin cewa na yi maguɗi.

Da yake mayar da martani, Ministan Yaɗa Labarai da Al’adu, Lai Mohammed ya zargi tsohon shugaban da gudanar da zaɓe “mafi muni a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya”.

“Duk da cewa yana bayyana kansa a matsayin dattijo mai kishin ƙasa, an san Obasanjo da goyon bayan wata jam’iyya da kuma yaudarar ‘yan Najeriya ta hanyar tauye musu abin da suka zaɓa,” kamar yadda wata sanarwa daga ma’aikatar yaɗa labarai ta ambato ministan na cewa.

Obasanjo ya ce ba wani sabon abu ba ne a zargi wasu daga cikin ma’aikatan hukumar zaɓen da suka gudanar da aikin da karɓar cin hanci kafin aika sakamako ta hanyar na’ura, abin da ya sa ake zargin an ƙirƙiri wani sakamkon ne.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man Kan Sayar da Farashin FeturNECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin Najeriya
X whatsapp