Home General Gwamnatin Tarayyar Nijeriya tayi Martani kan Bukatar Obasanjo

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya tayi Martani kan Bukatar Obasanjo

Gwamnatin Najeriya ta ce tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ba shi da “wata kimar” da zai nemi a dakatar da tattara sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da ake yi yanzu haka a ƙasar.

Gwamnatin ta mayar masa da martani ne bayan wasiƙar da ya rubuta a yammacin Litinin, yana mai neman Shugaba Muhammadu Buhari da shugaban hukumar zaɓe Mahmood Yakubu su soke sakamakon wasu yankuna da ya yi zargin cewa na yi maguɗi.

Da yake mayar da martani, Ministan Yaɗa Labarai da Al’adu, Lai Mohammed ya zargi tsohon shugaban da gudanar da zaɓe “mafi muni a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya”.

“Duk da cewa yana bayyana kansa a matsayin dattijo mai kishin ƙasa, an san Obasanjo da goyon bayan wata jam’iyya da kuma yaudarar ‘yan Najeriya ta hanyar tauye musu abin da suka zaɓa,” kamar yadda wata sanarwa daga ma’aikatar yaɗa labarai ta ambato ministan na cewa.

Obasanjo ya ce ba wani sabon abu ba ne a zargi wasu daga cikin ma’aikatan hukumar zaɓen da suka gudanar da aikin da karɓar cin hanci kafin aika sakamako ta hanyar na’ura, abin da ya sa ake zargin an ƙirƙiri wani sakamkon ne.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp