Home Labarai Za a daina ganin dogayen layuka a gidajen mai nan da ƴan...

Za a daina ganin dogayen layuka a gidajen mai nan da ƴan kwanaki – Mele Kyari

Shugaban Kamfanin mai na Najeriya, NNPCL, Mele Kyari ya bayyana fatan cewa layuka a gidajen sayar da mai a fadin kasar zai zama tarihi nan da kwana biyu masu zuwa.

Kyari ya shaida hakan ne a hirarsa da gidan Talabijin na Channels inda ya ce halin da aka shiga ba mai dorewa bane.

A cewarsa, baya tunanin dogayen layukan da ake kafawa zai kai har zuwa ranar Asabar.

Ya bayyana cewa akwai sama da lita miliyan 810 na man fetur a depo-depo da tankoki da kuma gidajen man da ke fadin Najeriya.

A ranar Litinin ne yayin jawabinsa bayan shan rantsuwar kama aiki, sabon shugaban kasa, Bola Tinubu ya ce zamanin biyan tallafin mai ya zo karshe, matakin da ya haifar da tashin farashin man fetur a sassan kasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp