Home SIYASA Tinubu ya kadu bisa abinda Ganduje ya yiwa kano – Kwankwaso

Tinubu ya kadu bisa abinda Ganduje ya yiwa kano – Kwankwaso

Tsohon gwamnan jihar Kano, Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ce shugaban kasa Bola Tinubu ne ya gayyaci su, shi da tsohon Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje kan rushe-rushen da ake yi a jihar.

Kwankwaso, wanda shi ne dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, ya ce Ganduje a matsayinsa na gwamna ya hana shi daga jihar Kano tsawon shekaru uku da rabi.

Da yake amsa tambayoyi daga manema labaran fadar shugaban kasa, Kwankwaso ya yi ikirarin cewa yawancin gine-ginen da aka rushe gwamnatin Ganduje ce ta sayar da su, ba bisa ka’ida ba, kuma shugaban kasa Tinubu ya kadu a lokacin da ya yi masa bayanin hakikanin abin da yasa ake rushe gine-ginen a halin yanzu.

Da aka tambaye shi ko ya gamsu da sanya bakin da shugaban kasa yayi akan rushe gine-ginen, sai ya ce: “Shugaban ya kadu Shin ba za ku yi mamakin ace muku wani ya sayar da Jami’a ba? Baku yi mamakin yadda ya rusa jami’a ba? Wato Daula Hotel, ga wadanda suka San Kano, ai kun san tsohur Daula, wadda aka rushe, to fa wata tsangaya ce a cikin Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Wudil, shin abun bai baku mamaki ba?” Inji Kwankwaso

“Shugaban kasar ya yi mamaki. Saboda bai sani ba. Ai lokacin Sallar idi ya karato da zaka yi Sallah a filin da kayi takaicin yadda aka mayar da wurin Sallah kasuwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp