Home DUNIYA Jagoran adawar Kamaru John Fru Ndi ya mutu

Jagoran adawar Kamaru John Fru Ndi ya mutu

Rahotanni daga Kamaru na bayyana cewa Jagoran jam’iyyar adawar kasar ta SDF John Fru Ndi ya mutu a daren litinin ya na da shekaru 81 bayan fama da jinya.

Jagoran adawar shi ne dan siyasa mafi dadewa da ya ci gaba da zama a jam’iyyar adawa tun zuwan siyasar jam’iyyu da dama a kasar.

John wanda ya yi fama da doguwar jinya shi ne dan siyasa daya tilo da ya shafe tsawon lokaci ya na watsi da tayin shugaban kasar Paul Biya wanda ya nemi ya shiga cikin gwamnatin don tafiya tare.

John Fru Ndi ya shafe tsawon shekaru ya na caccakar salon kamun ludayin gwamnatin Paul Biya shugaban da ya shafe shekaru 38 ya na mulkar kasar ta gabashin Afrika.

Zuwa yanzu dai ba a sanar da lokacin gudanar da jana’izar jagoran adawar mai shekaru 81 ba, sai dai tuni ‘yan kasar suka fara makokinsa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp