Home SIYASA Sanata Godswill Akpabio ya zama shugaban majalisar dattijai ta goma

Sanata Godswill Akpabio ya zama shugaban majalisar dattijai ta goma

Sanata Godswill Akpabio ya yi nasarar zama Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya ta goma, bayan zaɓaɓɓun ‘yan majalisar dattijai sun kaɗa ƙuri’a.

Akawun majalisar tarayya, Sani Tambuwal ne ya bayyana sakamakon zaɓen da ‘yan majalisar suka yi, inda ya ce Sanata Godswill Akpabio ya yi nasara da rinjayen ƙuri’a 63.

Ya dai kayar da abokin fafatawarsa, Sanata Abdul’aziz Yari ne wanda ya samu ƙuri’a 46.

Tuni Akawu Sani Tambuwal ya rantsar da sabon Shugaban Majalisar Dattijan, bayan ƙuri’un da ‘yan majalisa 107 suka kaɗa da safiyar Talata.

Matakin ya zo ne jim kaɗan da buɗe zaman majalisa ta goma a ranar Talata.

Magoya bayan sabon shugaban majalisar dattijan sun yi ta sowa a zauren majalisar inda suka je suna rungume Sanata Godswill Akpabio.

Da kammala zaɓen sabon shugaban majalisar dattijain kuma, yanzu an shiga matakin zaɓen mataimakinsa, inda Sanata Godswill Akpabio ya ɗare kan kujerar shugaban majalisar dattijai

Akawun Majalisar Dattijai ya ayyana Sanata Barau Jibrin a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattijai ta goma

Daga bisani, akawun majalisa ya rantsar da Sanata Barau Jibrin a matsayin halastaccen mataimakin shugaban majalisar dattijai.

Akpabio da Barau su ne ‘yan takarar da jam’iyyar APC mai mulki da Shugaba Bola Ahmed Tinubu suka mara wa baya don zama shugaban majalisar dattijai da mataimakinsa.

Tuni dai, akawun majalisar dattijai ya shiga rantsar da zaɓaɓɓun ‘yan majalisar dattijan.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp