Home SIYASA Sanata Godswill Akpabio ya zama shugaban majalisar dattijai ta goma

Sanata Godswill Akpabio ya zama shugaban majalisar dattijai ta goma

Sanata Godswill Akpabio ya yi nasarar zama Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya ta goma, bayan zaɓaɓɓun ‘yan majalisar dattijai sun kaɗa ƙuri’a.

Akawun majalisar tarayya, Sani Tambuwal ne ya bayyana sakamakon zaɓen da ‘yan majalisar suka yi, inda ya ce Sanata Godswill Akpabio ya yi nasara da rinjayen ƙuri’a 63.

Ya dai kayar da abokin fafatawarsa, Sanata Abdul’aziz Yari ne wanda ya samu ƙuri’a 46.

Tuni Akawu Sani Tambuwal ya rantsar da sabon Shugaban Majalisar Dattijan, bayan ƙuri’un da ‘yan majalisa 107 suka kaɗa da safiyar Talata.

Matakin ya zo ne jim kaɗan da buɗe zaman majalisa ta goma a ranar Talata.

Magoya bayan sabon shugaban majalisar dattijan sun yi ta sowa a zauren majalisar inda suka je suna rungume Sanata Godswill Akpabio.

Da kammala zaɓen sabon shugaban majalisar dattijain kuma, yanzu an shiga matakin zaɓen mataimakinsa, inda Sanata Godswill Akpabio ya ɗare kan kujerar shugaban majalisar dattijai

Akawun Majalisar Dattijai ya ayyana Sanata Barau Jibrin a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattijai ta goma

Daga bisani, akawun majalisa ya rantsar da Sanata Barau Jibrin a matsayin halastaccen mataimakin shugaban majalisar dattijai.

Akpabio da Barau su ne ‘yan takarar da jam’iyyar APC mai mulki da Shugaba Bola Ahmed Tinubu suka mara wa baya don zama shugaban majalisar dattijai da mataimakinsa.

Tuni dai, akawun majalisar dattijai ya shiga rantsar da zaɓaɓɓun ‘yan majalisar dattijan.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp