Home Labarai Za mu samar da sabbin wuraren kasuwanci a Kano – Abba gida-gida

Za mu samar da sabbin wuraren kasuwanci a Kano – Abba gida-gida

Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya yi alkawarin samar da kyakyawan wakilcin na ‘yan kasuwar jihar a majalisar zartarwa ta Kano.

Ta cikin wata sanarwar da mukaddashin mai magana da yawun gwamnan kano Hisham Habib ya aikowa PRNigeria, yace Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin ‘yan kasuwar Kano a gidan gwamnatin jihar.

Ya kuma ba su tabbacin kwamishinan kasuwanci da sauran mukamai da suka danganci yan kasuwa za su fito daga cikinsu don su sami wakilci a gwamnatinsa.

Ya ce gwamnatinsa za ta bunkasa harkokin kasuwanci a jihar, ya kuma tabbatar wa ‘yan kasuwar kudirinsa na tallafa wa harkokin kasuwanci dai-dai da zamani.

Ya ce gwamnati za ta kuma rage cunkoso a birnin kano, ta hanyar bude sabbin wuraren kasuwanci, ya kuma bukaci matasan ‘yan kasuwa da su yi amfani da damar wajen bada hadin kai don cigaban jihar kano.

A jawabinsa Mataimakin gwamnan jihar, Kwamared Aminu Abdussalam, ya jaddada kokarin gwamnati na ganin an dakile matsalar cin hanci da rashawa da jami’an hukumar kula da ababen hawa ta jihar da aka fi sani da KAROTA ke yi wadanda a zamanin gwamnatin da ta shude suka yi kaurin suna wajen karbar kudi a hannun yan kasuwar.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp