Home SIYASA Gwamnan jihar Kano Abba Kabir ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin shugabannin wasu hukumomi da ma’aikatun gwamnati.

Wannan na kunshe ta cikin wata Sanarwa da babban sakataren yada labaran gwaman, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria.

Wadanda aka nada din sune kamar haka.

1. Injiniya Ado Ibrahim Umar, Manajan Darakta na Kamfanin Wutar Lantarki na Kano (KHEDCO)

2. Alh. Auwalu Mukhtar Bichi, Manajan Daraktan Kamfanin Zuba Jari na kano.

3. Dr. Farouq Kurawa, Manajan Daraktan Hukumar KNARDA.

kafin ba shi wannan mukami , Dakta Kurawa shi ne Babban Sakataren gwamnan Kano wato (PPS) .

4. Dr. Tukur Dayyabu Minjibir, Manajan Daraktan Kamfanin Samar da Taki na Kano (KASCO).

5. Hussain Sarki Aliyu Madobi, Manajan Darakta na Cigaban aiyuka a Kano wato (SKP)

6. Sadiq Kura Muhammad, Manajan Darakta na gidan Zoo Kano (ZGK)

7. Injiniya Sani Bala, Manajan Daraktan Hukumar samar da wutar Lantarki a Karkara (REB)

8. Shamwilu Gezawa, hukumar samar da ruwan sha da tsaftar muhalli ta jihar Kano (RUWASA)

9. Alh. Tukur Bala Sagagi, Manajan Darakta na hukumar yawon bude ido ta jihar Kano

10. Alh. Yahaya Muhammad Idris Manajan Daraktan Kamfanin dab’i na Jihar Kano.

11. Adamu Yahaya, Mataimakin Manajin Darakta (DMD), Kamfanin dab’i na Kano

12. Abba El-mustapha, Sakataren zartarwa na Hukumar Tace Fina-Finai ta Jihar Kano

13. Dr. Muhammad S. Khalil, Babban Sakatare na Hukumar Kula da Sauyin Yanayi ta Jihar Kano (KN-WECCMA).

14. Dr. Dahir M. Hashim, Kodineta na Hukumar Kula da Sauyin yanayi ta Jihar Kano (KN-WECCMA).

Sanarwar na umartar Dukkanin wadanda aka nada dasu karbi ragamar aikin da aka dora musu nan take

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp