Home SIYASA Gwamnan jihar Kano Abba Kabir ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin shugabannin wasu hukumomi da ma’aikatun gwamnati.

Wannan na kunshe ta cikin wata Sanarwa da babban sakataren yada labaran gwaman, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria.

Wadanda aka nada din sune kamar haka.

1. Injiniya Ado Ibrahim Umar, Manajan Darakta na Kamfanin Wutar Lantarki na Kano (KHEDCO)

2. Alh. Auwalu Mukhtar Bichi, Manajan Daraktan Kamfanin Zuba Jari na kano.

3. Dr. Farouq Kurawa, Manajan Daraktan Hukumar KNARDA.

kafin ba shi wannan mukami , Dakta Kurawa shi ne Babban Sakataren gwamnan Kano wato (PPS) .

4. Dr. Tukur Dayyabu Minjibir, Manajan Daraktan Kamfanin Samar da Taki na Kano (KASCO).

5. Hussain Sarki Aliyu Madobi, Manajan Darakta na Cigaban aiyuka a Kano wato (SKP)

6. Sadiq Kura Muhammad, Manajan Darakta na gidan Zoo Kano (ZGK)

7. Injiniya Sani Bala, Manajan Daraktan Hukumar samar da wutar Lantarki a Karkara (REB)

8. Shamwilu Gezawa, hukumar samar da ruwan sha da tsaftar muhalli ta jihar Kano (RUWASA)

9. Alh. Tukur Bala Sagagi, Manajan Darakta na hukumar yawon bude ido ta jihar Kano

10. Alh. Yahaya Muhammad Idris Manajan Daraktan Kamfanin dab’i na Jihar Kano.

11. Adamu Yahaya, Mataimakin Manajin Darakta (DMD), Kamfanin dab’i na Kano

12. Abba El-mustapha, Sakataren zartarwa na Hukumar Tace Fina-Finai ta Jihar Kano

13. Dr. Muhammad S. Khalil, Babban Sakatare na Hukumar Kula da Sauyin Yanayi ta Jihar Kano (KN-WECCMA).

14. Dr. Dahir M. Hashim, Kodineta na Hukumar Kula da Sauyin yanayi ta Jihar Kano (KN-WECCMA).

Sanarwar na umartar Dukkanin wadanda aka nada dasu karbi ragamar aikin da aka dora musu nan take

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp