Home Labarai Rundunar ƴan sandan jahar Kano ta cafke mutane 62 da ake zargi...

Rundunar ƴan sandan jahar Kano ta cafke mutane 62 da ake zargi da aikata laifukan fashi da Makami a jihar

Rundunar ƴan sandan jahar Kano ta cafke mutane 62 da ake zargi da aikata laifukan fashi da Makami, Sata da aikata Daba da kuma Dilolin ƙwaya da dai sauransu.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne, ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar juma’a .

Sanarwar ta ce, an samu nasarar ƙwato muggan makamai guda 46 , sai codeine 253 , madarar Sukudayin 200 da kuma ƙulli-ƙulli na tabar wawi guda 1,802 da Babura biyu sa sauran muggan ƙwayoyi.

Kwamishinan ƴan sandan jahar Kano CP Muhammad Usaini Gumel ya godewa al’ummar jahar bisa haɗin kai da goyon bayan sa suke bawa rundunar a koda yaushe.

Kiyawa ya ƙara da cewa, nasarar ra biyo bayan miƙa wuya da wasu matasa 99 suka yi sa ake zargi da aiyukan Faɗan Fada a cikin birnin Kano, waɗanda suka Tuba tare da ajiye makamansu.

Rundunar ƴan sandan jahar ta sanya tukwicin Naira dubu ɗari 300,000. ga dukkan wanda ya bauyar da bayanan sirri kan wasu matasa uku da suka ƙi miƙa wuya dan a cafke su.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp