Home Labarai Rundunar ƴan sandan jahar Kano ta cafke mutane 62 da ake zargi...

Rundunar ƴan sandan jahar Kano ta cafke mutane 62 da ake zargi da aikata laifukan fashi da Makami a jihar

Rundunar ƴan sandan jahar Kano ta cafke mutane 62 da ake zargi da aikata laifukan fashi da Makami, Sata da aikata Daba da kuma Dilolin ƙwaya da dai sauransu.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne, ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar juma’a .

Sanarwar ta ce, an samu nasarar ƙwato muggan makamai guda 46 , sai codeine 253 , madarar Sukudayin 200 da kuma ƙulli-ƙulli na tabar wawi guda 1,802 da Babura biyu sa sauran muggan ƙwayoyi.

Kwamishinan ƴan sandan jahar Kano CP Muhammad Usaini Gumel ya godewa al’ummar jahar bisa haɗin kai da goyon bayan sa suke bawa rundunar a koda yaushe.

Kiyawa ya ƙara da cewa, nasarar ra biyo bayan miƙa wuya da wasu matasa 99 suka yi sa ake zargi da aiyukan Faɗan Fada a cikin birnin Kano, waɗanda suka Tuba tare da ajiye makamansu.

Rundunar ƴan sandan jahar ta sanya tukwicin Naira dubu ɗari 300,000. ga dukkan wanda ya bauyar da bayanan sirri kan wasu matasa uku da suka ƙi miƙa wuya dan a cafke su.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp