Home General Mun Kama ‘Yan dabar da Wani Dan Siyasa ya tura ƙunci da...

Mun Kama ‘Yan dabar da Wani Dan Siyasa ya tura ƙunci da Tsanyawa – CP Gumel.

Rundunar ‘yan Sandan Kano ta tabbatar da kama wasu ‘yan Daba, da ake zargin wani Dan Siyasa ya tura wurin Zaɓen cike gurbi ,na ƙananan Hukumomin ƙunci da Tsanyawa.

Kwamishinan ‘Yan Sandan kano CP. Muhammad Hussaini Gumel ne ya bayyana hakan, Jim kadan da kama gungun matasan a lokacin da suke zagayen yadda Zaɓen cike gurbin yake gudana.

CP Gumel ya ƙara da cewa, tuni ‘Yan daban suka kama sunan ɗan Siyasa me Suna Gwarmai, a matsayin Wanda ya turo su domin su je su tayar da hankali a wurin Zaɓen cike gurbin na Ƙunci da Tsanyawa.

‘Yan Sandan sun kama ‘yan dabar da makamai ne, samfurin Adduna, Gorori, Gariyo, da dai sauran su, a dai-dai lokacin da suke kan hanyar su ta shiga garin Ƙunci.

Gumel yace zasu Binciki Dan Siyasar domin tabbatar da gaskiyar lamarin dama gurfanar dashi a gaban kuliya, matukar zargin yayi ƙarfi a kansa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp