Home General Mun Kama ‘Yan dabar da Wani Dan Siyasa ya tura ƙunci da...

Mun Kama ‘Yan dabar da Wani Dan Siyasa ya tura ƙunci da Tsanyawa – CP Gumel.

Rundunar ‘yan Sandan Kano ta tabbatar da kama wasu ‘yan Daba, da ake zargin wani Dan Siyasa ya tura wurin Zaɓen cike gurbi ,na ƙananan Hukumomin ƙunci da Tsanyawa.

Kwamishinan ‘Yan Sandan kano CP. Muhammad Hussaini Gumel ne ya bayyana hakan, Jim kadan da kama gungun matasan a lokacin da suke zagayen yadda Zaɓen cike gurbin yake gudana.

CP Gumel ya ƙara da cewa, tuni ‘Yan daban suka kama sunan ɗan Siyasa me Suna Gwarmai, a matsayin Wanda ya turo su domin su je su tayar da hankali a wurin Zaɓen cike gurbin na Ƙunci da Tsanyawa.

‘Yan Sandan sun kama ‘yan dabar da makamai ne, samfurin Adduna, Gorori, Gariyo, da dai sauran su, a dai-dai lokacin da suke kan hanyar su ta shiga garin Ƙunci.

Gumel yace zasu Binciki Dan Siyasar domin tabbatar da gaskiyar lamarin dama gurfanar dashi a gaban kuliya, matukar zargin yayi ƙarfi a kansa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp