Home General Hukumar ‘Yan Sanda tace baza ta bi Umarnin Gwamnatin Kano ba.

Hukumar ‘Yan Sanda tace baza ta bi Umarnin Gwamnatin Kano ba.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bayyana umarnin ta na bijerewa umarnin gwamnan jihar na fidda tsohon sarkin kano Aminu Ado Bayero daga Gidan sarki na Nassarawa.

Idan za’a iya tunawa a ranar Alhamis gwamnan jihar Kano ta bakin kwamishinan Shari’a na jihar Haruna Dederi ya bawa kwamishinan ‘yan sandan jihar Usaini Gumel kan ya fidda tsohon sarkin daga gidan bisa hukuncin kotu tarayya dake jihar kano da ya tabbatar da dokar da majalisar jihar kano ta samar a 2024.

Da ya ke ganawa ta wayar tarho da wakilin jaridar Punch a ranar Juma’a, kwamishinan ‘yan sandan yace bin umarnin gwamnan na fitar da tsohon sarkin tamkar riga malam masallaci ne.

Yace gwamnatin dai da ta bayar da umarnin itace ta shigar da kara gaba gaban babbar kotun jiha akan batun na fitar da sarkin wanda ktoun zata zauna a ranar litinin 24 Yuni 2024.

Tun bayan umarnin gwamantin jihar ta Kano, aka wayi gari da sake girke jami’an ‘yan sanda a harabar gidan sarkin na Nassarawa, inda tsohon sarkin kano Aminu Ado Bayero yace Gwamnatin jihar na tsrae da shi a ciki.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp