Home General Hukumar ‘Yan Sanda tace baza ta bi Umarnin Gwamnatin Kano ba.

Hukumar ‘Yan Sanda tace baza ta bi Umarnin Gwamnatin Kano ba.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bayyana umarnin ta na bijerewa umarnin gwamnan jihar na fidda tsohon sarkin kano Aminu Ado Bayero daga Gidan sarki na Nassarawa.

Idan za’a iya tunawa a ranar Alhamis gwamnan jihar Kano ta bakin kwamishinan Shari’a na jihar Haruna Dederi ya bawa kwamishinan ‘yan sandan jihar Usaini Gumel kan ya fidda tsohon sarkin daga gidan bisa hukuncin kotu tarayya dake jihar kano da ya tabbatar da dokar da majalisar jihar kano ta samar a 2024.

Da ya ke ganawa ta wayar tarho da wakilin jaridar Punch a ranar Juma’a, kwamishinan ‘yan sandan yace bin umarnin gwamnan na fitar da tsohon sarkin tamkar riga malam masallaci ne.

Yace gwamnatin dai da ta bayar da umarnin itace ta shigar da kara gaba gaban babbar kotun jiha akan batun na fitar da sarkin wanda ktoun zata zauna a ranar litinin 24 Yuni 2024.

Tun bayan umarnin gwamantin jihar ta Kano, aka wayi gari da sake girke jami’an ‘yan sanda a harabar gidan sarkin na Nassarawa, inda tsohon sarkin kano Aminu Ado Bayero yace Gwamnatin jihar na tsrae da shi a ciki.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp