Home General Sojojin Nijeriya sun kashe dan fashin daji Alhaji Kachalla Ragas a jihar...

Sojojin Nijeriya sun kashe dan fashin daji Alhaji Kachalla Ragas a jihar Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta ce jami’an tsaron haɗin gwiwa sun kashe wani jagoran ‘yan fashin daji mai suna Alhaji Kachalla Ragas tare da wasu abokan harkarsa da dama.

Wata sanarwa da Kwamashinan Tsaron jihar Samuel Aruwan ya fitar a yau Juma’a ta ce dakarun rundunar Operation Whirl Punch ne suka yi nasarar kashe shi bayan hare-haren da suka kai ta sama a ƙaramar hukumar Giwa da ke jihar ta arewa maso yammacin Najeriya.

“Hare-haren ta sama da ƙasa sun yi nasarar kashe ‘yanbindiga da yawa tare da shugabanninsu a dajin Yadi da ke yankin Bula,” in ji sanarwar.

Ya ƙara da cewa an kai harin ne bayan samun bayanan sirri cewa ‘yanbindigar “za su yi wani taro don kitsa mummunan aiki, inda daga baya masu leƙen asiri suka hangi gungun mutum bakwai zuwa 10 ɗauke da makamai”.

“Cikin waɗanda aka kashe har da Alhaji Kachalla Ragas, wanda abokin Buharin Yadi ne wanda shi ma aka kashe kwanan nan,” a cewar sanarwar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp