Home General Sojojin Nijeriya sun kashe dan fashin daji Alhaji Kachalla Ragas a jihar...

Sojojin Nijeriya sun kashe dan fashin daji Alhaji Kachalla Ragas a jihar Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta ce jami’an tsaron haɗin gwiwa sun kashe wani jagoran ‘yan fashin daji mai suna Alhaji Kachalla Ragas tare da wasu abokan harkarsa da dama.

Wata sanarwa da Kwamashinan Tsaron jihar Samuel Aruwan ya fitar a yau Juma’a ta ce dakarun rundunar Operation Whirl Punch ne suka yi nasarar kashe shi bayan hare-haren da suka kai ta sama a ƙaramar hukumar Giwa da ke jihar ta arewa maso yammacin Najeriya.

“Hare-haren ta sama da ƙasa sun yi nasarar kashe ‘yanbindiga da yawa tare da shugabanninsu a dajin Yadi da ke yankin Bula,” in ji sanarwar.

Ya ƙara da cewa an kai harin ne bayan samun bayanan sirri cewa ‘yanbindigar “za su yi wani taro don kitsa mummunan aiki, inda daga baya masu leƙen asiri suka hangi gungun mutum bakwai zuwa 10 ɗauke da makamai”.

“Cikin waɗanda aka kashe har da Alhaji Kachalla Ragas, wanda abokin Buharin Yadi ne wanda shi ma aka kashe kwanan nan,” a cewar sanarwar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp