Home General An sake zaben Tinubu shugaban ECOWAS

An sake zaben Tinubu shugaban ECOWAS

An sake zabar Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu a matsayin Shugaban Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) a wa’adi na biyu.

Tinubu wanda wa’adin mulkinsa zai kare ranar 9 ga watan Yunin 2024, an sake zaben sa ne bisa hukuncin shuwagabancin kungiyar a yayin gudanar da taron ta karo na 65 a Abuja a ranar Lahadi.

A yayin da yake jawabi bayan sake zaben nasa, Bola Tinubu ya ce, “Na karbi wannan mukami domin ci gaba da habaka wannan tafiya ta dimukuradiyya, kuma mu hidimtawa wannan yankin da muka gada daga hannun magabatanmu”.

Wasu rahotanni daga fadar shugaban kasa dai sun ce an sake zaben Tinubu a zango na biyu na shugabancin kungiyar ta ECOWAS domin ya ci gaba da jan ragamarta.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasashen Nijar, Mali da Burkina Faso, waɗanda a baya suka sanar da ficewa daga ƙungiyar suka ce sam ba su da sha’awar dawowa cikinta.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp