Home General An sake zaben Tinubu shugaban ECOWAS

An sake zaben Tinubu shugaban ECOWAS

An sake zabar Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu a matsayin Shugaban Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) a wa’adi na biyu.

Tinubu wanda wa’adin mulkinsa zai kare ranar 9 ga watan Yunin 2024, an sake zaben sa ne bisa hukuncin shuwagabancin kungiyar a yayin gudanar da taron ta karo na 65 a Abuja a ranar Lahadi.

A yayin da yake jawabi bayan sake zaben nasa, Bola Tinubu ya ce, “Na karbi wannan mukami domin ci gaba da habaka wannan tafiya ta dimukuradiyya, kuma mu hidimtawa wannan yankin da muka gada daga hannun magabatanmu”.

Wasu rahotanni daga fadar shugaban kasa dai sun ce an sake zaben Tinubu a zango na biyu na shugabancin kungiyar ta ECOWAS domin ya ci gaba da jan ragamarta.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasashen Nijar, Mali da Burkina Faso, waɗanda a baya suka sanar da ficewa daga ƙungiyar suka ce sam ba su da sha’awar dawowa cikinta.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp