Home Labarai Gwamnatin jihar Borno ta sanya dokar hana fita a jihar

Gwamnatin jihar Borno ta sanya dokar hana fita a jihar

Gwamnatin jihar Borno da ke arewacin Najeriya ta ayyana dokar hana fita ra awa 24 a faɗin jihar.

A cikin wata sanarwa, wadda ta samu sa hannun mai magana da yawun rundunar ƴansandan Najeriya a jihar, ASP Nahum Kenneth, ta ce an ɗauki matakin hakan ne domin tabbatar da tsaro bisa ga la’akari da halin da ake ciki.

Sanarwar ta ce: “A ƙoƙarin tabbatar da doka da oda, gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, bayan ganawa da shugabannin hukumomin tsaro a jihar, ya ga wajibcin ayyana dokar hana fita ta awa 24 wadda za ta fara aiki nan take.”

Sanarwar ta ƙara da cewa “an ga buƙatar hakan ne ta hanyar la’akari da fashewar da aka samu wadda ta yi sanadiyyar mutuwar mutum 16 da raunata wasu da dama a jihar.”

Wannan dai na zuwa ne a rana ta farko bayan fara zanga-zangar da matasa suka shirya domin nuna fushi kan matsin rayuwa a ƙasar.

Matasa sun fito a biranen faɗin ƙasar a safiyar Alhamis, inda suke ɗauke da alluna waɗanda ke ɗauke da ƙorafe-ƙorafensu masu nasaba da matsin rayuwa da rashin tsaro.

Sai dai an samu rahotanni na tashin hatsaniya a wasu jihohin ƙasar, inda rahotanni suka bayyana cewa an harbi kimanin mutum uku a jihar Kano, yayin da aka jefa wa masu zanga-zanga barkono mai sa hawaye a yankuna da dama, har da Abuja, babban birnin ƙasar.

A jihar Borno ma lamarin ya so ya dagule a lokacin da aka samu hargitsi a unguwar Bulunkutu, inda jami’an ƴansanda suka jefa barkono mai sa hawaye kan masu zanga-zanga.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp