Home Labarai Gwamnatin jihar Borno ta sanya dokar hana fita a jihar

Gwamnatin jihar Borno ta sanya dokar hana fita a jihar

Gwamnatin jihar Borno da ke arewacin Najeriya ta ayyana dokar hana fita ra awa 24 a faɗin jihar.

A cikin wata sanarwa, wadda ta samu sa hannun mai magana da yawun rundunar ƴansandan Najeriya a jihar, ASP Nahum Kenneth, ta ce an ɗauki matakin hakan ne domin tabbatar da tsaro bisa ga la’akari da halin da ake ciki.

Sanarwar ta ce: “A ƙoƙarin tabbatar da doka da oda, gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, bayan ganawa da shugabannin hukumomin tsaro a jihar, ya ga wajibcin ayyana dokar hana fita ta awa 24 wadda za ta fara aiki nan take.”

Sanarwar ta ƙara da cewa “an ga buƙatar hakan ne ta hanyar la’akari da fashewar da aka samu wadda ta yi sanadiyyar mutuwar mutum 16 da raunata wasu da dama a jihar.”

Wannan dai na zuwa ne a rana ta farko bayan fara zanga-zangar da matasa suka shirya domin nuna fushi kan matsin rayuwa a ƙasar.

Matasa sun fito a biranen faɗin ƙasar a safiyar Alhamis, inda suke ɗauke da alluna waɗanda ke ɗauke da ƙorafe-ƙorafensu masu nasaba da matsin rayuwa da rashin tsaro.

Sai dai an samu rahotanni na tashin hatsaniya a wasu jihohin ƙasar, inda rahotanni suka bayyana cewa an harbi kimanin mutum uku a jihar Kano, yayin da aka jefa wa masu zanga-zanga barkono mai sa hawaye a yankuna da dama, har da Abuja, babban birnin ƙasar.

A jihar Borno ma lamarin ya so ya dagule a lokacin da aka samu hargitsi a unguwar Bulunkutu, inda jami’an ƴansanda suka jefa barkono mai sa hawaye kan masu zanga-zanga.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp