Home Labarai Gwamnatin Kano ta magantu kan halin da ake ciki a jihar

Gwamnatin Kano ta magantu kan halin da ake ciki a jihar

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce ba za su saurarawa duk masu kokarin tayar da fitina da sunan zanga-zanga a fadin jihar kano ba.

Gwamnan ya furta haka ne yau a gidan Gwamnati Lokacin da yake karbar takardar korafi daga wasu jagororin al’umma kan dalilin da ya sa Suka fara gudanar da zanga Zanga a yau Alhamis.

Gwamnan ya kara da cewa duk da yake kudin tsarin mulkin kasa ya bayar da dama gudanar dazanga-zanga lumana ,amma gwamnati ba za ta zuba Ido wasu bata gari suyi amfani da ita ba wajen sace-sace kone-kone da fasa shagunan alumma, in da ya ce jami,an tsaro za su yi aiki ba sani ba sabo ga duk Wanda aka kama da hannu a ciki.

Gwamnan ya yabawa jami’an tsaro bisa yadda Suka jajirce wajen kakkabe batagari da ke Neman tayar da fitina a jihar kano.

Ya Kuma yabawa kungiyar da ta kawo takardar kokenta da cewa zai Jagorancin wasu daga cikin al’ummar kano har zuwa fadar Shugaban kasa don Mika sakonsu kan irin halin matsin da alumma ke ciki.

daga bisani  Gwamnan ya ja hankalin ‘ya siyasa da su guji yin amfani da bata gari don cimma bukatunsu

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp