Home AFIRKA Fararen hula 10 sun mutu sakamakon harin ƴan ta’adda a Burkina Faso

Fararen hula 10 sun mutu sakamakon harin ƴan ta’adda a Burkina Faso

Wasu da ake zargi yan ta’adda masu ikirarin jihadi ne sun kashe fararen hula 10 a wata kasuwa da ke arewacin ƙasar ƙarshen makon da ya gabata, kamar yadda jami’an yankin su ka bayyana a ranar Talata.

Wasu mazauna lardin Gnagna inda lamarin ya faru ssun ce ƴan ta’addan sun farmaki garin ne da yammacin Lahadi, inda su ka kashe mutane tare da raunata da dama.

Wani jami’in asibiti a yankin ya ce yana da matuƙar wahala a tantance adadin waɗanda su ka mutu, amma ya ce  akalla mutane 10 sun mutu, kana 50 su ka jikkata.

Ganau sun ce maharan sun sun shiga garin ne kuma su ka fara harbi kan uwa da wabi, inda su ka tarwatsa jama’a, har su ka fara fasa shaguna su na sata.

Ƙasar da ke yankin yammacin nahiyar Afrika tana fama da matsalar ƴan ta’adda masu ikirarin jihadi da su ka kwarara daga makwafciyarta Mali tun daga shekarar 2015.

Dubban fararen hula, sojoji da yan sanda ne aka kashe, lamarin da ya fusata wasu hafsoshin soji har su ka yi juyin mulki  a shekarar 2022.

Sama da mutane dubu 26 ne su ka mutu sakamakon hare-haren ƴan ta’adda a Burkina Faso tun daga shekarar 2015, fiye da dubu 6 daga cikin su a wannan shekarar aka kashe su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp