Home AFIRKA Fararen hula 10 sun mutu sakamakon harin ƴan ta’adda a Burkina Faso

Fararen hula 10 sun mutu sakamakon harin ƴan ta’adda a Burkina Faso

Wasu da ake zargi yan ta’adda masu ikirarin jihadi ne sun kashe fararen hula 10 a wata kasuwa da ke arewacin ƙasar ƙarshen makon da ya gabata, kamar yadda jami’an yankin su ka bayyana a ranar Talata.

Wasu mazauna lardin Gnagna inda lamarin ya faru ssun ce ƴan ta’addan sun farmaki garin ne da yammacin Lahadi, inda su ka kashe mutane tare da raunata da dama.

Wani jami’in asibiti a yankin ya ce yana da matuƙar wahala a tantance adadin waɗanda su ka mutu, amma ya ce  akalla mutane 10 sun mutu, kana 50 su ka jikkata.

Ganau sun ce maharan sun sun shiga garin ne kuma su ka fara harbi kan uwa da wabi, inda su ka tarwatsa jama’a, har su ka fara fasa shaguna su na sata.

Ƙasar da ke yankin yammacin nahiyar Afrika tana fama da matsalar ƴan ta’adda masu ikirarin jihadi da su ka kwarara daga makwafciyarta Mali tun daga shekarar 2015.

Dubban fararen hula, sojoji da yan sanda ne aka kashe, lamarin da ya fusata wasu hafsoshin soji har su ka yi juyin mulki  a shekarar 2022.

Sama da mutane dubu 26 ne su ka mutu sakamakon hare-haren ƴan ta’adda a Burkina Faso tun daga shekarar 2015, fiye da dubu 6 daga cikin su a wannan shekarar aka kashe su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp