Home General Gwamnatin Najeriya na shirin cire harajin VAT a kan magunguna

Gwamnatin Najeriya na shirin cire harajin VAT a kan magunguna

Hukumomi a Najeriya sun ce sun soma wani yunƙuri na cire harajin VAT da kuma harajin shigo da kaya a kan magunguna da kuma na’urorin lafiya.

Sanarwar da ma’aikatar kiwon lafiyar ƙasar ta fitar, ta ce a yanzu haka an kusan kammala tsarin da yadda shugaban ƙasa zai bayar da umarni a kai.

“Matakin zai tabbatar da cewa hukumar tara haraji ta Najeriya – FIRS da kuma hukumar kwastam sun aiwatar da umarnin na cire harajin VAT a kan magani da kuma na’urorin lafiya,” in ji sanarwar.

A tsakiyar wannan shekarar, ministan lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate ya sanar da cewa shugaba Tinubu ya sanya hannu a kan dokar samar da magani da sirinji da sauran kayayyakin lafiya a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp