Home General Matsin rayuwa: Ana zaluntarku kun kasa komai, Amaechi ya yi kira ga...

Matsin rayuwa: Ana zaluntarku kun kasa komai, Amaechi ya yi kira ga matasa da su yi zanga-zanga

Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya bayyana rashin jin dadinsa da yadda ƴan Nijeriya su ka zauna suna kallo an jefa su cikin mawuyacin hali na tattalin arziki.
Da ya ke magana a wata hira da gidan talabijin na ABN TV, Amaechi ya yi tambaya kan dalilin da ya sa ‘yan Najeriya ba sa kwarmata halin wuya da su ke ciki, yana mai nuni da hauhawar farashin kayayyaki da kuma rashin iya biyan bukatun yau da kullum kamar man fetur.
Tsohon gwamnan na Rivers ya ce shi kan sa ba zai iya siyan dizal ba.
Amaechi ya ce yana sa ran matasa za su mamaye tituna daban-daban su yi zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa.
Ya ce: “Ina fushi da ’yan kasa. Na sha fadi hakan. Za ka ga gungun mutane suna sace maku kudi suna talauta ku, ba za ku iya siyan mai da komai ba.
“Ya kamata mutane su yi fushi. Kamata ya yi a yi zanga-zanga. Ba ma zanga-zangar adawa da kowa ba sai ga ’yan siyasa. A rika cewa ‘ba za mu zabe kuba” in ji shi.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp