Home General Matsin rayuwa: Ana zaluntarku kun kasa komai, Amaechi ya yi kira ga...

Matsin rayuwa: Ana zaluntarku kun kasa komai, Amaechi ya yi kira ga matasa da su yi zanga-zanga

Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya bayyana rashin jin dadinsa da yadda ƴan Nijeriya su ka zauna suna kallo an jefa su cikin mawuyacin hali na tattalin arziki.
Da ya ke magana a wata hira da gidan talabijin na ABN TV, Amaechi ya yi tambaya kan dalilin da ya sa ‘yan Najeriya ba sa kwarmata halin wuya da su ke ciki, yana mai nuni da hauhawar farashin kayayyaki da kuma rashin iya biyan bukatun yau da kullum kamar man fetur.
Tsohon gwamnan na Rivers ya ce shi kan sa ba zai iya siyan dizal ba.
Amaechi ya ce yana sa ran matasa za su mamaye tituna daban-daban su yi zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa.
Ya ce: “Ina fushi da ’yan kasa. Na sha fadi hakan. Za ka ga gungun mutane suna sace maku kudi suna talauta ku, ba za ku iya siyan mai da komai ba.
“Ya kamata mutane su yi fushi. Kamata ya yi a yi zanga-zanga. Ba ma zanga-zangar adawa da kowa ba sai ga ’yan siyasa. A rika cewa ‘ba za mu zabe kuba” in ji shi.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp