Home General Gwamnatin Najeriya ta ce ba ta da hannu wajen ƙarin kuɗin fetur...

Gwamnatin Najeriya ta ce ba ta da hannu wajen ƙarin kuɗin fetur a ƙasar.

Hoton Tinubu

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tarayya ba ta da hannu wajen ƙarin kuɗin mai na baya-bayan nan.

“Dalilan da suka kawo wannan ƙarin farashin sun haɗa da rikicin gabas ta tsakiya, saboda ya haifar da tashin farashin mai a kasuwannin duniya.”

Ministan ya yi kira ga ƴan Najeriya da su ci gaba da ba NNPCL da gwamnatin haɗin kai, “Gwamnati za ta yi amfani da kuɗin tallafin da aka cire wajen inganta fannin lafiya da ilimi, tsaro.”

Kamfanin mai na Najeriya NNPCL ya yi ƙarin kuɗin fetur a ranar Laraba, inda farashin ya tashi daga naira 897 zuwa 1,030 kowace lita a Abuja, yayin da a jihar Lagos ya tashi daga naira 855 zuwa 998.

A jihohin arewa maso gabas, man ya koma naira 1,070 a yankin kudu maso yamma, naira 1,025 jihohin kudu maso gabas ya kai naira 1,045.

Matakin ya janyo cece-kuce a tsakanin ƴan Najeriya, inda suke ci gaba da neman shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wani kan tashin farashin man.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp