Home General Gwamnatin Najeriya ta ce ba ta da hannu wajen ƙarin kuɗin fetur...

Gwamnatin Najeriya ta ce ba ta da hannu wajen ƙarin kuɗin fetur a ƙasar.

Hoton Tinubu

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tarayya ba ta da hannu wajen ƙarin kuɗin mai na baya-bayan nan.

“Dalilan da suka kawo wannan ƙarin farashin sun haɗa da rikicin gabas ta tsakiya, saboda ya haifar da tashin farashin mai a kasuwannin duniya.”

Ministan ya yi kira ga ƴan Najeriya da su ci gaba da ba NNPCL da gwamnatin haɗin kai, “Gwamnati za ta yi amfani da kuɗin tallafin da aka cire wajen inganta fannin lafiya da ilimi, tsaro.”

Kamfanin mai na Najeriya NNPCL ya yi ƙarin kuɗin fetur a ranar Laraba, inda farashin ya tashi daga naira 897 zuwa 1,030 kowace lita a Abuja, yayin da a jihar Lagos ya tashi daga naira 855 zuwa 998.

A jihohin arewa maso gabas, man ya koma naira 1,070 a yankin kudu maso yamma, naira 1,025 jihohin kudu maso gabas ya kai naira 1,045.

Matakin ya janyo cece-kuce a tsakanin ƴan Najeriya, inda suke ci gaba da neman shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wani kan tashin farashin man.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp