Home General Gwamnatin Najeriya ta ce ba ta da hannu wajen ƙarin kuɗin fetur...

Gwamnatin Najeriya ta ce ba ta da hannu wajen ƙarin kuɗin fetur a ƙasar.

Hoton Tinubu

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tarayya ba ta da hannu wajen ƙarin kuɗin mai na baya-bayan nan.

“Dalilan da suka kawo wannan ƙarin farashin sun haɗa da rikicin gabas ta tsakiya, saboda ya haifar da tashin farashin mai a kasuwannin duniya.”

Ministan ya yi kira ga ƴan Najeriya da su ci gaba da ba NNPCL da gwamnatin haɗin kai, “Gwamnati za ta yi amfani da kuɗin tallafin da aka cire wajen inganta fannin lafiya da ilimi, tsaro.”

Kamfanin mai na Najeriya NNPCL ya yi ƙarin kuɗin fetur a ranar Laraba, inda farashin ya tashi daga naira 897 zuwa 1,030 kowace lita a Abuja, yayin da a jihar Lagos ya tashi daga naira 855 zuwa 998.

A jihohin arewa maso gabas, man ya koma naira 1,070 a yankin kudu maso yamma, naira 1,025 jihohin kudu maso gabas ya kai naira 1,045.

Matakin ya janyo cece-kuce a tsakanin ƴan Najeriya, inda suke ci gaba da neman shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wani kan tashin farashin man.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp