Home AFIRKA Mahukuntan Chadi sun sabunta gargaɗi kan yiwuwar sake fuskantar ambaliya

Mahukuntan Chadi sun sabunta gargaɗi kan yiwuwar sake fuskantar ambaliya

Mahukuntan Chadi sun fitar da sanarwar gargaɗi da ke buƙatar jama’a su ɗauki matakan kariya da kuma yin taka-tsan-tsan don kaucewa asarar rayuka bayan ambaliyar da ta sake kunno kai a tsakar birnin N’Djamena sakamakon mamakon ruwan sama da kuma tumbatsar kogin Chari.

A ɓangare guda bayanai sun ce kogin Logone ya yi tumbatsa mafi ƙololuwa da ba a ga irinta cikin shekaru 30 zuwa 40 da suka gabata ba, wanda ya sanya matakin da ya sanya fargabar sake tsanantar ambaliyar ƙasar wadda kawo yanzu ta hallaka mutane 576 tare da raba wasu miliyan 1 da dubu 900 da matsugunansu tun bayan farowarta a watan Yulin da ya gabata.

Masana sun yi gargaɗin cewa wasu sassa na Chadi ka iya fuskantar zabtarewar laka ƙari kan ambaliyar da ake ci gaba da gani tsawon makwanni.

Ƙasashe da dama a yankunan yammaci da tsakiyar Afrika ne suka yi fam ada ambaliyar ruwa a damunar bana, sai dai halin da ake ciki a Chadi ya fi ko’ina tsananta lura da yadda matsalar ta shafi miliyoyin iyalai.

Shugabar hukumar kula da albarkatun ruwa ta Chadi Sakine Youssouf ta ce tumbatsar kogin Logone ya wuce yadda ake tsammani inda a jiya Laraba ya kai mita 8.18 fiye da yadda aka yi tsammanin tumbatsar shi.

Tuni dai Firaminista Maye Halina ya jagoranci wani taron gaggawa na masu ruwa da tsaki don ɗaukar matakan da za su baiwa jama’a kariya daga ƙaƙƙarfar ambaliyar da ake hasashe da kuma wadda tuni ta shafi yankuna 17 cikin 23 da ƙasar ke da su ciki har da fadar gwamnati.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp