Home AFIRKA Mahukuntan Chadi sun sabunta gargaɗi kan yiwuwar sake fuskantar ambaliya

Mahukuntan Chadi sun sabunta gargaɗi kan yiwuwar sake fuskantar ambaliya

Mahukuntan Chadi sun fitar da sanarwar gargaɗi da ke buƙatar jama’a su ɗauki matakan kariya da kuma yin taka-tsan-tsan don kaucewa asarar rayuka bayan ambaliyar da ta sake kunno kai a tsakar birnin N’Djamena sakamakon mamakon ruwan sama da kuma tumbatsar kogin Chari.

A ɓangare guda bayanai sun ce kogin Logone ya yi tumbatsa mafi ƙololuwa da ba a ga irinta cikin shekaru 30 zuwa 40 da suka gabata ba, wanda ya sanya matakin da ya sanya fargabar sake tsanantar ambaliyar ƙasar wadda kawo yanzu ta hallaka mutane 576 tare da raba wasu miliyan 1 da dubu 900 da matsugunansu tun bayan farowarta a watan Yulin da ya gabata.

Masana sun yi gargaɗin cewa wasu sassa na Chadi ka iya fuskantar zabtarewar laka ƙari kan ambaliyar da ake ci gaba da gani tsawon makwanni.

Ƙasashe da dama a yankunan yammaci da tsakiyar Afrika ne suka yi fam ada ambaliyar ruwa a damunar bana, sai dai halin da ake ciki a Chadi ya fi ko’ina tsananta lura da yadda matsalar ta shafi miliyoyin iyalai.

Shugabar hukumar kula da albarkatun ruwa ta Chadi Sakine Youssouf ta ce tumbatsar kogin Logone ya wuce yadda ake tsammani inda a jiya Laraba ya kai mita 8.18 fiye da yadda aka yi tsammanin tumbatsar shi.

Tuni dai Firaminista Maye Halina ya jagoranci wani taron gaggawa na masu ruwa da tsaki don ɗaukar matakan da za su baiwa jama’a kariya daga ƙaƙƙarfar ambaliyar da ake hasashe da kuma wadda tuni ta shafi yankuna 17 cikin 23 da ƙasar ke da su ciki har da fadar gwamnati.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp