Home AFIRKA Algeria ta haramtawa kamfanonin Faransa shigar mata da alkama

Algeria ta haramtawa kamfanonin Faransa shigar mata da alkama

Algeria ta tsame kamfanonin Faransa daga jerin masu shigar mata da alkama matakin da ke sake tabbatar da farraƙar da ke tsakanin ƙasar ta arewacin Afrika ta uwar goyonta da ta yi mata mulkin mallaka.

Shekaru 3 kenan ana tafka rikicin diflomasiyya tsakanin Algiers da Paris kuma ko a farkon rikicin sai da Algeria ta dakatar da kamfanonin na Faransa daga shigar mata da alkama na tsawon watanni gabanin dawo da su bakin aiki daga bisani.

Wasu majiyoyi sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, wani sabin rikici ne ya kunno kai tsakanin ƙasashen biyu.

Bayanai na nuna cewa wannan dakatarwa ta baya-bayan nan ka iya ƙarfafa Rasha wadda ita ke shigar da alkama ga tarin ƙasashen gabas ta tsakiya ta hanyar amfani da tekun Black Sea.

Algeria na matsayin ƙasa mafi sayen alkamar da Faransa ke nomawa, wanda kuma shi ne wani ɓangaren na tattalin arziƙin ƙasar ta Turai, kai tsaye dakatar da hada-hadar da ke tsakaninsu zai shafi tattalin arzƙin kamfanoni da dama a ƙasar haka zalika ƙananun manoma dama tarin ma’aikata.

Ana dai ganin matakin Faransa na nuna goyon baya ga ci gaba da kasancewar yankin yammacin ƙarƙashin ikon Morocco ya fusata Algeria ƙasar da ta shafe tsawon lokaci ta na fafutukar ƴancin ƴan Polisario.

Har yanzu dai ma’aikatar kasuwancin Faransa a ƙetare ba ta yi tsokaci kan matakin na Algeria ba, wanda ta sanar tun a jiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp