Home AFIRKA Algeria ta haramtawa kamfanonin Faransa shigar mata da alkama

Algeria ta haramtawa kamfanonin Faransa shigar mata da alkama

Algeria ta tsame kamfanonin Faransa daga jerin masu shigar mata da alkama matakin da ke sake tabbatar da farraƙar da ke tsakanin ƙasar ta arewacin Afrika ta uwar goyonta da ta yi mata mulkin mallaka.

Shekaru 3 kenan ana tafka rikicin diflomasiyya tsakanin Algiers da Paris kuma ko a farkon rikicin sai da Algeria ta dakatar da kamfanonin na Faransa daga shigar mata da alkama na tsawon watanni gabanin dawo da su bakin aiki daga bisani.

Wasu majiyoyi sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, wani sabin rikici ne ya kunno kai tsakanin ƙasashen biyu.

Bayanai na nuna cewa wannan dakatarwa ta baya-bayan nan ka iya ƙarfafa Rasha wadda ita ke shigar da alkama ga tarin ƙasashen gabas ta tsakiya ta hanyar amfani da tekun Black Sea.

Algeria na matsayin ƙasa mafi sayen alkamar da Faransa ke nomawa, wanda kuma shi ne wani ɓangaren na tattalin arziƙin ƙasar ta Turai, kai tsaye dakatar da hada-hadar da ke tsakaninsu zai shafi tattalin arzƙin kamfanoni da dama a ƙasar haka zalika ƙananun manoma dama tarin ma’aikata.

Ana dai ganin matakin Faransa na nuna goyon baya ga ci gaba da kasancewar yankin yammacin ƙarƙashin ikon Morocco ya fusata Algeria ƙasar da ta shafe tsawon lokaci ta na fafutukar ƴancin ƴan Polisario.

Har yanzu dai ma’aikatar kasuwancin Faransa a ƙetare ba ta yi tsokaci kan matakin na Algeria ba, wanda ta sanar tun a jiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp