Home AFIRKA Algeria ta haramtawa kamfanonin Faransa shigar mata da alkama

Algeria ta haramtawa kamfanonin Faransa shigar mata da alkama

Algeria ta tsame kamfanonin Faransa daga jerin masu shigar mata da alkama matakin da ke sake tabbatar da farraƙar da ke tsakanin ƙasar ta arewacin Afrika ta uwar goyonta da ta yi mata mulkin mallaka.

Shekaru 3 kenan ana tafka rikicin diflomasiyya tsakanin Algiers da Paris kuma ko a farkon rikicin sai da Algeria ta dakatar da kamfanonin na Faransa daga shigar mata da alkama na tsawon watanni gabanin dawo da su bakin aiki daga bisani.

Wasu majiyoyi sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, wani sabin rikici ne ya kunno kai tsakanin ƙasashen biyu.

Bayanai na nuna cewa wannan dakatarwa ta baya-bayan nan ka iya ƙarfafa Rasha wadda ita ke shigar da alkama ga tarin ƙasashen gabas ta tsakiya ta hanyar amfani da tekun Black Sea.

Algeria na matsayin ƙasa mafi sayen alkamar da Faransa ke nomawa, wanda kuma shi ne wani ɓangaren na tattalin arziƙin ƙasar ta Turai, kai tsaye dakatar da hada-hadar da ke tsakaninsu zai shafi tattalin arzƙin kamfanoni da dama a ƙasar haka zalika ƙananun manoma dama tarin ma’aikata.

Ana dai ganin matakin Faransa na nuna goyon baya ga ci gaba da kasancewar yankin yammacin ƙarƙashin ikon Morocco ya fusata Algeria ƙasar da ta shafe tsawon lokaci ta na fafutukar ƴancin ƴan Polisario.

Har yanzu dai ma’aikatar kasuwancin Faransa a ƙetare ba ta yi tsokaci kan matakin na Algeria ba, wanda ta sanar tun a jiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp