Home AFIRKA Algeria ta haramtawa kamfanonin Faransa shigar mata da alkama

Algeria ta haramtawa kamfanonin Faransa shigar mata da alkama

Algeria ta tsame kamfanonin Faransa daga jerin masu shigar mata da alkama matakin da ke sake tabbatar da farraƙar da ke tsakanin ƙasar ta arewacin Afrika ta uwar goyonta da ta yi mata mulkin mallaka.

Shekaru 3 kenan ana tafka rikicin diflomasiyya tsakanin Algiers da Paris kuma ko a farkon rikicin sai da Algeria ta dakatar da kamfanonin na Faransa daga shigar mata da alkama na tsawon watanni gabanin dawo da su bakin aiki daga bisani.

Wasu majiyoyi sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, wani sabin rikici ne ya kunno kai tsakanin ƙasashen biyu.

Bayanai na nuna cewa wannan dakatarwa ta baya-bayan nan ka iya ƙarfafa Rasha wadda ita ke shigar da alkama ga tarin ƙasashen gabas ta tsakiya ta hanyar amfani da tekun Black Sea.

Algeria na matsayin ƙasa mafi sayen alkamar da Faransa ke nomawa, wanda kuma shi ne wani ɓangaren na tattalin arziƙin ƙasar ta Turai, kai tsaye dakatar da hada-hadar da ke tsakaninsu zai shafi tattalin arzƙin kamfanoni da dama a ƙasar haka zalika ƙananun manoma dama tarin ma’aikata.

Ana dai ganin matakin Faransa na nuna goyon baya ga ci gaba da kasancewar yankin yammacin ƙarƙashin ikon Morocco ya fusata Algeria ƙasar da ta shafe tsawon lokaci ta na fafutukar ƴancin ƴan Polisario.

Har yanzu dai ma’aikatar kasuwancin Faransa a ƙetare ba ta yi tsokaci kan matakin na Algeria ba, wanda ta sanar tun a jiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp