Home AFIRKA Hukumomin Libya na ci gaba da tsare ƴan Najeriya da Nijar sama...

Hukumomin Libya na ci gaba da tsare ƴan Najeriya da Nijar sama da 900 – Rahotanni

Wasu rahotanni daga kasar Libiya na cewa, wani bangare na hukumomin kasar, sun kama wasu ƴan kasashen Afrirka bakin haure bakaken fata yawanci ƴan asalin kasar Jumhuriyar Nijar da Najeriya sama da 900.

Sama da wata daya da ake rike da wadannan mutane sai dai har zuwa yanzu babu wani cikaken bayani game da inda suke.

Tuni wasu da suka galabaita daga ciki suka fara mutuwa.

Wani daga wadanda suka tsira a lokacin da aka kai samamen da jami’an tsaro suka kai a lokacin da suka kama ƴan Afirkar ya shaida wa BBC cewe ” Ranar 6 ga watan Satumba ne jami’an tsaron suka kai samame, suka kama mutanen Nijar da Najeriya, ” Nima ina cikin mutanen amman na gudu ne shiyasa ba a kama ni ba, amman sun dauki mutanen da suka kai 500 a lokacin.”

“Daga baya cikin wadanda suka kama din basu anshe amsu wayoyi ba, sune suka kira suke fadin cewa adadin mutanen da aka kama sun kai 900 kuma yawancinsu ƴan Nijar ne” cewar mutumin.

Wasu daga cikin farar hula na Nijar din na ci gaba da kira ga hukumomin ƙasar da su sanya baki kan lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp