Home Labarai Sojojin Nijeriya sun kubutar da Yara mata 12 daga hannun mayakan ISWAP...

Sojojin Nijeriya sun kubutar da Yara mata 12 daga hannun mayakan ISWAP a Borno

Sojojin  Nijeriya karkashin dakarun rundunar OPERATON HADIN KAI sun sami nasarar kubutar da yara mata 12 da mayakan kungiyar boko haram suka yi garkuwa da su a kauyen Mussa dake karamar hukumar Askira/Uba dake jihar Borno a Arewa aso gabashin Nijeriya.

Mayakan boko haram sun yi garkuwa da yaran ne a lokacin da suke girbe amfanin gonarsu a ranar 23 ga watan Nuwamba, wanda kuma suka shaki iskan ‘yanci a ranar 29 ga watan na Nuwamba bayan abinda dakarun sojin suka bayyana samun bayanan sirri da kuma ayyukan kakkabe matsalar tsaro a yakin kudancin jihar.

Ta cikin wata sanarwa da rundunar sojin ta aikewa PRNigeria ta bayyana cewa wadanda aka kubutar din dake mata ne kuma suna karbar kulawar likitoci domin tallafawa lfiyarsu kamar yadda ya kamata. Wanda nan ba da jimawa ba za’a sadasu da iyalansu.

Yaran da aka kubutar suna hadar da  Fatima Shaibu (17), Fatima Umaru (15), Hauwa Abubakar (18), Saliha Muhammed (15), Sadiya Umaru (17), Amira Babel (15), Zara Adamu (17), Nana Shaibu (15), Zainab Musa (18), Zainab Muhammed (17), Jamila Saidu (15), and Hauwa Hamidu (17).

Rundunar Sojin ta yabawa dakarun nata bisa namijin kokarin da uke nunawa a yaki da matsalar tsaro a yankin, sannan ta bukaci Al’ummar dake jihar su sake sanya idanu gami da taimakawa jami’an tsar da bayanan sirri.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp