Home Labarai Sojojin Nijeriya sun kubutar da Yara mata 12 daga hannun mayakan ISWAP...

Sojojin Nijeriya sun kubutar da Yara mata 12 daga hannun mayakan ISWAP a Borno

Sojojin  Nijeriya karkashin dakarun rundunar OPERATON HADIN KAI sun sami nasarar kubutar da yara mata 12 da mayakan kungiyar boko haram suka yi garkuwa da su a kauyen Mussa dake karamar hukumar Askira/Uba dake jihar Borno a Arewa aso gabashin Nijeriya.

Mayakan boko haram sun yi garkuwa da yaran ne a lokacin da suke girbe amfanin gonarsu a ranar 23 ga watan Nuwamba, wanda kuma suka shaki iskan ‘yanci a ranar 29 ga watan na Nuwamba bayan abinda dakarun sojin suka bayyana samun bayanan sirri da kuma ayyukan kakkabe matsalar tsaro a yakin kudancin jihar.

Ta cikin wata sanarwa da rundunar sojin ta aikewa PRNigeria ta bayyana cewa wadanda aka kubutar din dake mata ne kuma suna karbar kulawar likitoci domin tallafawa lfiyarsu kamar yadda ya kamata. Wanda nan ba da jimawa ba za’a sadasu da iyalansu.

Yaran da aka kubutar suna hadar da  Fatima Shaibu (17), Fatima Umaru (15), Hauwa Abubakar (18), Saliha Muhammed (15), Sadiya Umaru (17), Amira Babel (15), Zara Adamu (17), Nana Shaibu (15), Zainab Musa (18), Zainab Muhammed (17), Jamila Saidu (15), and Hauwa Hamidu (17).

Rundunar Sojin ta yabawa dakarun nata bisa namijin kokarin da uke nunawa a yaki da matsalar tsaro a yankin, sannan ta bukaci Al’ummar dake jihar su sake sanya idanu gami da taimakawa jami’an tsar da bayanan sirri.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp