Home SIYASA Gwamna Ortom ya Caccaki APC Kan Yadda Tsofaffi Suke Shirin Tsayawa Takara...

Gwamna Ortom ya Caccaki APC Kan Yadda Tsofaffi Suke Shirin Tsayawa Takara a Jam’iyyar

Gwamna Ortom ya Caccaki APC Kan Yadda Tsofaffi Suke Shirin Tsayawa Takara a Jam’iyyar

Gwamna Samuel Ortom na Jihar Binuwai ya shawarci ‘yan Najeriyan da suka zarce shekaru 70 da haihuwa da su hakura da takarar shugaban kasa.

Kamar yadda ya ce, ya kamata su bai wa masu jin a jika da ilimin zamani wuri don su amshi ragamar shugabancin kasa.

Gwamnan ya yi maganar ne jiya yayin da Bukola Saraki, Bala Mohammed da Tambuwal suka kai masa ziyara don jin matakan da PDP ta dauka na tsayar da dan takara.

Jihar Benue – Gwamnan Jihar Benue, Samuel Ortom ya ba ‘yan Najeriya da suka wuce shekaru 70 shawarar dakatawa daga tsayawa takarar shugaban kasa.

A cewarsa, zai fi dacewa su ba wa masu kananun shekaru da kuma ilimi irin na zamani damar shugabanci, Vanguard ta ruwaito.

A jiya, gwamnan ya yi wannan bayanin ne yayin da ya amshi tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, Gwamna Aminu Tambuwal na Jihar Sokoto da Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi, wadanda suka je tuntubarsa don sanin shirin jam’iyyar PDP na tsayar da dan takara.

Ya caccaki APC saboda yadda tsofaffi suke shirin tsayawa takara a jam’iyyar

Kamar yadda Vanguard ta nuna, gwamnan ya ce:

“Ina so in shawarci ‘yan Najeriya dangane da hadin kai. Sanin kowa ne cewa a baya an samu tarin nasarori saboda dunkulewar ‘yan Najeriya wuri guda. Suna kai ziyara har ga ‘yan uwansu na kudu yayin da suke nuna burinsu na tsayawa takara. Ya kamata mu yi aiki tare. Duk da PDP jam’iyyar adawa ce, amma muna da dokokinmu.

“Shiyasa yanzu haka PDP a shirye take da ta ceto Najeriya ta kuma kara gina ta. Yanzu ku duba mutane ukun nan, a jiya (ranar Lahadi), akwai wani mutumin kirki daga Jihar Ribas, Gwamna Wike, wanda ya zo nan Jihar Binuwai yana neman tsayawa takarar shugaban kasa.

“Ku kalli wadannan matasan, ku hada su da tsofaffin can na APC da take son su tsaya takarar shugaban kasa a zamanin nan da ake ciki. Ya kamata a ba matasa dama. Ba zan kira suna ba, amma duk wanda ya wuce shekaru 70 kuma yake son ya tsaya takara, ba ya yiwa Najeriya fatan alheri.”

Yayin jawabi, tsohon shugaban majalisar dattawa, Saraki ya ce ya zo Jihar Binuwai ne don su tattauna sannan su san shirin da PDP take yi na tsayar da dan takarar shugaban kasa.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp