Home SIYASA Na Janye  Daga Neman Takarar  Shugbancin Jam’iyyar APC – Ali Modu Sheriff

Na Janye  Daga Neman Takarar  Shugbancin Jam’iyyar APC – Ali Modu Sheriff

Na Janye  Daga Neman Takarar  Shugbancin Jam’iyyar APC – Ali Modu Sheriff

 

Tsohon gwamnan Borno da ke arewa maso gabas, Ali Modu Sheriff, ya ce ya janye daga takarar neman shugbancin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya.

Modu Sheriff ya faɗa wa BBC Hausa cewa ya janye takarar ce saboda biyayya ga Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

“Shugaban ƙasa na son shugaban jam’iyya ya fito daga Arewa ta Tsakiya. Shugabanmu ne, babanmu ne, duk abin da yake so shi za mu yi. Ni ba na jayayya da iyayena a kowane fanni,” in ji shi.

Matakin tsohon gwamnan na zuwa ne bayan jam’iyyar ta ce ta ware wa shiyyar arewa ta tsakiya muƙamin shugaba na ƙasa yayin ganawar da gwamnoninta suka yi da Shugaba Buhari a watan Fabarairu.

An ware wa shiyyoyin Arewa muƙaman da na Kudu suka riƙe a cikin shekara takwas da suka wuce, su ma na Kudu haka, a cewar Gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai.

Bisa wannan tsari ne jam’iyyar za ta zaɓi ssabbin shugabanninta a babban taron da za ta gudanar ranar 26 ga watan Maris.

‘Matakin da zan ɗauka nan gaba’

Ali Modu Sharif ya gode wa dukkan mutanen da suka goya masa baya”, amma ya ce ba zai daina siyasa ba.

“Ina jira daga nan zuwa Juma’a, idan jam’iyya ta ce kowane yanki zai iya tsayawa takara ina nan,” a cewarsa.

Da aka tambaye shi ko zai bar siyasa, sai ya amsa da cewa: “Ba zan bar siyasa ba. Don me zan bar siyasa?

“Ba zan nemi wani muƙami ba sai na shugaban jam’iyya saboda na taimaka wa jam’iyyarmu mai girma.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp