Home Labarai E-TICKETING: Gwamnatin Tarayya ta Sami Karin Miliyan 3 na Harajin Jirgin Kasa

E-TICKETING: Gwamnatin Tarayya ta Sami Karin Miliyan 3 na Harajin Jirgin Kasa

Ministan Sufuri Rotimi Amaechi yace an dakatar da Hukumar Lura da Sufurin Jiragen Kasa ta Nijeriya (NRC) daga sayar da tikitin hawa Jirgin ga matafiya.

Ya bayyanna hakan ne yayin da yake gabatar da takardar sahelewar saida tikitin da za’a sayar ta yanar gizo (E-ticketing) na Legas zuwa Ibadan dana Itakpe zuwa Warri ga hukumar ICRC

Ameachi Yace an dauki wannan mataki ne domin dakile cin hanci da rashawa da kuma barazanar rashin tsaro da Hukumar ta NRC ke fuskanta.

Ya kara da cewa tun bayan kaddamar da wannan tsari na E-Ticketing kudin shigar da ake samu ya rubanya.

PRNigeria ta rawaito Ameachi na cewa daukar wannan mataki ya zama waji ne kasancewar yadda matsalar rashin tsaro ke kara addabar hanyoyi a Nijeriya

“Duk da dai baza mu iya magance matsalar rashin tsaron da cin hanci da rashawa dari bisa dari ba, amma hakan zai rage matsalar rashin tsaron da muke fuskanta”

“yanzu gwamnatin Tarayya taga Alfanun wannan tsari, ta hanyar kara samun kudin shiga daga miliyan dari daya duk wata zuwa miliyan dari 4.”

Idan za’a iya tunawa PRNigeria ta rawaito cewa wasu ‘Yan Bindiga sun dasa abun fashewa a kan titin jirgin kasa daga Abuja zuwa kaduna Abinda yayi sanadiyyar mutuwar mutane da dama tare da batan wasu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp