Home Labarai GIDAUNIYAR QATAR DA TALLAFAWAR GIDAUNIYAR MALAM INUWA TA RABAWA MARAYU KAYAN SALLAH...

GIDAUNIYAR QATAR DA TALLAFAWAR GIDAUNIYAR MALAM INUWA TA RABAWA MARAYU KAYAN SALLAH A JIHAR JIGAWA

Gidauniyar ayyukan jinƙai da taimakon al’umma ta ƙasar Qatar ta gudanar da rabon tallafin kayan sallah ɗinkakku ga yara marayu mata da maza sama da mutum (100) a Jihar Jigawa bisa tallafawar gidauniyar ba da agaji, taimako, jinƙai da ayyukan alkhairi ta Malam Inuwa, wacce mai girma shugaban hukumar (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE) ya kafa.

Taron rabon kayan wanda aka gudanar a ɗakin taro na makarantar koyon aikin jinya da ungurzoma da ke Haɗejia , ya gudana ne a ƙarƙashin jagorancin jagoran tawagar gidauniyar ta ƙasar Qatar, Shaik Hamdi da shugabannin gidauniyar Malam Inuwa, ƙarƙashin jagorancin Dakta Hussaini Baban.

Da yake jawabi yayin rabon kayan sallar, jagoran tawagar gidauniyar ta Ƙasar Qatar, Sheik Hamdi ya yabawa gidauniyar Malam Inuwa da fadar Mai Martaba Sarkin Haɗejia a bisa haɗin kai da ƙarfafa gwiwar da su ke ba su a duk lokacin da su ka nufaci gudanar da ire-iren waɗannan ayyukan alheri.

Shi ma a nasa jawabin, shugaban gidauniyar ta Malam Inuwa, Dakta Usaini Yusuf Baban ya bayyana godiya da addu’ar fatan alkhairi ga gidauniyar bisa wannan ayyuka da su ke yi, inda ya jadda aniyarsu ta cigaba da marawa ayyukan gidauniyar baya duba da yadda ita ma gidauniyar ta ke ƙoƙari kan wannan aiki inda ko da a wannan wata na Ramadan ta yi rabon tallafin shinkafa ga marayu ɗari-ɗari a kowacce ƙaramar hukuma tare da raba kayan sallah ga marayu da dama.

Taron ya samu halartar sakataren kwamitin marayu na Jihar Jigawa Shaik Abdulƙadir Zakar, da na’ibin limamin masarautar Haɗejia, Malam Umar Hamza Abbas da sauran masu ruwa da tsaki.

Yara marayun da su ka amfana da wannan tallafi sun bayyana farin cikinsu matuƙa da godiya bisa wannan abin alkhairi da aka yi musu gami da addu’ar Allah Ya ba da lada.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp