Home General Gobara :Fashewar Gas Ta Yi Sanadiyyar Jakkatar Mutane 20 a Jihar Kano

Gobara :Fashewar Gas Ta Yi Sanadiyyar Jakkatar Mutane 20 a Jihar Kano

Wasu rahotannin daga jihar Kano sun tabbatar da sake samun fashewa a shagon sayar da gas ɗin girki a wata unguwa da ke cikin garin Kano, lamarin da ya jikkata mutum 20 da ƙona shaguna da dama.

Ko da yake dai wannan adadi na mutum 20 ganau ne suka tabbatarwa da PRNigeria ba hukumomin da abun ya shafa ba, duk da cewa wani bayani ya tabbatar da cewa jami’an tsaro a jihar na ganawa yanzu haka kan lamarin.

Wannan dai na zuwa ne makwanni bayan samun irin wannan fashewar a titin Aba dake unguwar Sabon Gari a Kano, inda mutum 9 da suka mutu baya ga wadanda suka jikkata.

Ko da yake a wannan lokacin an yi ta samun bayanai masu cin karo da juna, rundunar ‘yan sanda na cewa tukunyar gas ce, ganau kuma na cewa bam ne. duk da cewa daga bisani rundunar ‘yan sanda ta fito ta bayyana cewa wani mai sayar da kayan hada bam ne ya tashi da shi.

Rahotanni dai na cewa iftila’in na wannan lokaci ya faru ne a unguwar Sheka, Karshen-Kwalta.

Sai dai ganau sun ce mutum guda ya rigamu gidan gaskiya

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp