Home Labarai Hadirin Mota Yayi Sandiyyar Mutuwar Mutum 7 Tare da Jikkata 5

Hadirin Mota Yayi Sandiyyar Mutuwar Mutum 7 Tare da Jikkata 5

Hukumar kiyaye Aukuwar hadurra reshen jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar mutum 7 kuma mutum 5 sun jikkata, yayin da wasu motoci 2 sukayi taho mu gama a kan babbar hanyar Lokoja zuwa Abuja a ranar Alhamis.

Kwamandan shiyya na na hukumar ta FRSC, Stephen Dawulung ne ya tabbatar aukuwar lamarin ga manema labarai a garin lokoja ranar Juma’a.

Yace lamarin ya faru ne yayi da wata mota Bus kirar Toyota Hiece tayi gaba da gaba da wata mota kirar Daf a garin Akpanya dake daura da koton karfe a hanyar Abuja zuawa lokoja.

“yayin da motocin 2 sukay taho mu gama, mutum 7 suka mutu nan take, inda mutum 5 kuma suka sami raunika a sassan jikin su.

“Jami’an mu sun garzawa wajen da lamarin ya faru bayan samun rahoto, nan suka shiga ikin taimako nan kuwa suka taimaki musamman wadanda suka ji rauni da taimakon gaggawa.

“tuni dai an garzaya da wadanda suka ji raunin zuwa asibitin koton karfe, inda ake lura da lafiyar tasu, an kuma an ajje wadanda suka mutu a warin ajiyar gawarwaki na asibiti (Mortuary) kamar yadda ya bayyana.

Dawulung ya bayyana cewa hadarin ya auku ne sakamakon Gudun wuce sa’a da matuka Ababan hawan ke yi a yayin da suke tsaka da tuki.

Daga bisani ya bukaci Al’umma, musamman matuka Ababan hawa da su gujewa tafiyar dare, tare da yin gudun wuce sa’a, yayin tukun kuma su tabbatar sun bi dokoki da ka’idojin hanya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp