Home Labarai Hadirin Mota Yayi Sandiyyar Mutuwar Mutum 7 Tare da Jikkata 5

Hadirin Mota Yayi Sandiyyar Mutuwar Mutum 7 Tare da Jikkata 5

Hukumar kiyaye Aukuwar hadurra reshen jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar mutum 7 kuma mutum 5 sun jikkata, yayin da wasu motoci 2 sukayi taho mu gama a kan babbar hanyar Lokoja zuwa Abuja a ranar Alhamis.

Kwamandan shiyya na na hukumar ta FRSC, Stephen Dawulung ne ya tabbatar aukuwar lamarin ga manema labarai a garin lokoja ranar Juma’a.

Yace lamarin ya faru ne yayi da wata mota Bus kirar Toyota Hiece tayi gaba da gaba da wata mota kirar Daf a garin Akpanya dake daura da koton karfe a hanyar Abuja zuawa lokoja.

“yayin da motocin 2 sukay taho mu gama, mutum 7 suka mutu nan take, inda mutum 5 kuma suka sami raunika a sassan jikin su.

“Jami’an mu sun garzawa wajen da lamarin ya faru bayan samun rahoto, nan suka shiga ikin taimako nan kuwa suka taimaki musamman wadanda suka ji rauni da taimakon gaggawa.

“tuni dai an garzaya da wadanda suka ji raunin zuwa asibitin koton karfe, inda ake lura da lafiyar tasu, an kuma an ajje wadanda suka mutu a warin ajiyar gawarwaki na asibiti (Mortuary) kamar yadda ya bayyana.

Dawulung ya bayyana cewa hadarin ya auku ne sakamakon Gudun wuce sa’a da matuka Ababan hawan ke yi a yayin da suke tsaka da tuki.

Daga bisani ya bukaci Al’umma, musamman matuka Ababan hawa da su gujewa tafiyar dare, tare da yin gudun wuce sa’a, yayin tukun kuma su tabbatar sun bi dokoki da ka’idojin hanya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp