Home Labarai Mutum 9 Sun Mutu Yayin Da Dama Suka Jikkata Sakamakon Hadari A...

Mutum 9 Sun Mutu Yayin Da Dama Suka Jikkata Sakamakon Hadari A Gombe

road safety

Kwamandan shiyya na hukumar kiyaye haddurata jihar Gombe Felix Theman ya tabbatar da mutuwar mutum 9 wasu mutum 11 kuma suka jikkata a sakamakon wani hari da ya auku a yammacin ranar laraba.
Theman ya bayyana cewa hadarin ya auku ne a mahadar Bomala dake gombe ta kudu da misalign karfe 8 na yamma, sakamakon Birki daya shayewa a wata motar tirela da take dauke da jarkokin man girki.
Yace hadarin ya rutsa da mutum 20, inda likitoci suka tabbatar da mutuwar mutum 9, mutane 11 kuma suka sami muggana raunika, sakamakon hadirin.
Ya tabbatar da cewa wadanda suka jikka an garzaya da su Asibitin koyarwa na FTHG dake Gombedomin basu kulawar data dace.
Daga bisani Kwamandan Shiyyar ya bukaci matuka Ababan hawa da su gujewa yin gudun wuce sa’a, musamman a lokacin da suka shigo cikin Al’umma, yace ya kamata ace tafiya a cikin mutane ta kasance kilomita 40 cikin sa’a guda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp