Home Labarai Dan Bindiga 1 Ya Mutu ‘Yan Sanda Sun Kama 3 A Jihar...

Dan Bindiga 1 Ya Mutu ‘Yan Sanda Sun Kama 3 A Jihar Benue

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Benue sun sami nasarar kame wasu da ake zargin na da hannu a kai harin garin Igama na karamar hukuma Okpokwu dake jihar.

ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar yan sandan jihar Catherine Anene ya fita a ranar Alhamis, yace wadanda ake zargin dai ya mutu ne sakamakon raunin harbi da ya samu a gwamzawar da jami’an ‘yan sandada gugun ‘yan bindigar.

Wakilin mu ya rawaito mana cewa maharan sun afka garin a yammacin ranar lahadi inda suka halaka mutum 15, daga bisani suka banka wuta a gidajen Al’ummar garin.

Ta cikin sanarwa rundunar ‘yan sandan ta tabbatar da jibge jami’anta hadin gwuiwa da sauran jami’an tsaro, domin bincika lungu da sako na dazukan dake yankin.

“A ranar 15 ga watan Yuni, misalin karfe 5 na safe, maharan dake makale a cikin daji, sun yi artabu da ‘yan sanda wanda ya kai ga an cafke Umar Nuhu, Dauda Alhaji, Musa Dako da Umaru Alhaji Sale.

“Daya daga cikin wadanda ake zargin mai suna Musa Dako ya samu raunuka kuma an kwantar da shi a Asibitin St. Mary’s dake Okpoga inda a karshe ya mutu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp