Home Labarai Dan Bindiga 1 Ya Mutu ‘Yan Sanda Sun Kama 3 A Jihar...

Dan Bindiga 1 Ya Mutu ‘Yan Sanda Sun Kama 3 A Jihar Benue

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Benue sun sami nasarar kame wasu da ake zargin na da hannu a kai harin garin Igama na karamar hukuma Okpokwu dake jihar.

ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar yan sandan jihar Catherine Anene ya fita a ranar Alhamis, yace wadanda ake zargin dai ya mutu ne sakamakon raunin harbi da ya samu a gwamzawar da jami’an ‘yan sandada gugun ‘yan bindigar.

Wakilin mu ya rawaito mana cewa maharan sun afka garin a yammacin ranar lahadi inda suka halaka mutum 15, daga bisani suka banka wuta a gidajen Al’ummar garin.

Ta cikin sanarwa rundunar ‘yan sandan ta tabbatar da jibge jami’anta hadin gwuiwa da sauran jami’an tsaro, domin bincika lungu da sako na dazukan dake yankin.

“A ranar 15 ga watan Yuni, misalin karfe 5 na safe, maharan dake makale a cikin daji, sun yi artabu da ‘yan sanda wanda ya kai ga an cafke Umar Nuhu, Dauda Alhaji, Musa Dako da Umaru Alhaji Sale.

“Daya daga cikin wadanda ake zargin mai suna Musa Dako ya samu raunuka kuma an kwantar da shi a Asibitin St. Mary’s dake Okpoga inda a karshe ya mutu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp