Home Labarai Alkalin Alkalan Nijeriya Yayi Murabus

Alkalin Alkalan Nijeriya Yayi Murabus

Alkalin Alkalan Nijeriya (CJN) mai shari’a Muhammad Tanko yayi murabus daga mukamin sa na babban mai shari’a a kotun koli.

Rahotannin sun bayyana cewa ya yi murabus din ne sakamakon rashin lafiya  da yake fama da ita.

Ana sa rana daga na zuwa ko wanne lokaci za’a maye gurbin sa da mai shari’a olukayode Ariwoola , wannan da ke matsayin mafi girma bayan mai shari’a Mary Odili wadda tayi ritaya  12 ga watan mayun bayan ta cika shekaru 70 a matsayin mukaddashi.

An dai hafi Mai shari’a Muhammad a garin Doguwa, dake karamar hukumar Gaide ta jihar Bauchi a ranar 31, Disamban 1953.

Ya halarci makaranatr Firamare ta Giade daga 1961 zuwa 1968, inda ya tafi zuwa sakandire ta Azare a shekarar 1969 zuwa 1973, daga bisani  ya zuwa makarantar Abdullahi Bayero University College, kano inda yayi karatun share fagen shiga jami’a na IJMB daga shekarar 1975 zuwa 1976, bayan ya sami nasarar ne ya sammi gurbin karatu a jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria daga shekara 1976 zuwa 1980, ya kuma halarci kwalejin  koyan aikin shari’a daga shekarar 1980 zuwa 1981.

Domin Karin karatu ya koma zuwa jami’ar Ahmadu Bello dake Zari’a, inda ya sake samun digiri na 2 a fannin shari’a (LLM) a wani tsari na wucin gadi daga shekarar1982 zuwa 1984.

Saboda sake samun gogewa a fannin ya dora dai a jami’ar ta Ahmadu Bello domin samu digirin na 3 (PhD) a fanin shari’a duk dai a tsarin wucin gadi.

Daga bisani shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya rantsar da shi a matsayin Alkalin Alkalan kasar a watan Janairun 2019, bayan dakatar da mai shari’a Walter Onnoghen.

Bisa doka dai dukkan babban Alkalin kotun koli a Nijeriya wajibi ne yayi murabus da zarar ya kai shekara 70 a duniya.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp