Home Labarai ‘Yan Bindiga Sunyi garkuwa Da DPO A Jihar Kaduna

‘Yan Bindiga Sunyi garkuwa Da DPO A Jihar Kaduna

‘Yan bindiga masu garkuwa da mutane sun kama sabon baturen ‘yan sanda da aka tura karamar hukumar birnin Gwari dake jihar kaduna.

Anyi garkuwa da baturen ‘yan sandan ne akan babbar hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari da misalin karfe 9 na safiyar ranar litinin a yayin da yake kokarin zuwa inda aka turashi domin kama aiki.

Wata majiya ta sai dawa PRNigeria cewa baturen ‘yan Sandan (DPO) na kan hanyar sa zuwa birnin Gwari masu garkuwar suka kama shi, sai kawo yanzu ba’a tabbatar da ko yayi tafiya shi kadai bane ko akasin haka.

Kawo yanzu dai hukumar ‘yan sandan jihar na tattara bayanai domin fidda sanarwa a hukumance, kamar yadda kakakin Rundunar ‘yan sandan jihar ta Kaduna Muhammad Jalige ya bayyana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp