Home Labarai An bukaci Jami’an yada labaran (PROs) na Hukumar (NCS) Da Suke...

An bukaci Jami’an yada labaran (PROs) na Hukumar (NCS) Da Suke Yin Amfani da Kayan Aikin Yada Labarai Na Zamani

An bukaci Jami’an yada labaran (PROs) na hukumar hana fasa kwauri na Nijeriya (NCS) da suke yin amfani da kayan aikin yada labarai na zamani.

An yi wannan kira ne a yayin wani taron horaswa da hukumar ta shirya wa masu Magana da yawunta.

Da yake Magana a wajen taron horaswa kwamandan dake lora da sashen horas da jami’an Kwastam (CTC) dake Ikeja, Kwantorola Kalamu Ayinde Aremu, ya bayyana cewa yin amfani da sabuwar fasahar zamani zai taimaka matuka wajen sake daga darajar hukumar.

Kakakin hukaumar na kasa DC Timi Bomodi yace, an gadanar da wannan horaswa domin  baiwa jami’an sashin hulda da jama’a na hukumar horon da zai taimaka musu wajen gudanar da ayyukan su yadda ya dace da zamani.

Da yake gabatar da Makala mai take “Effective Public Communication” a yayin taron horaswar Babban mai tace Labarai na jaridar PRNigeria, Yushau Shuaib ya bayyana cewa an sami gagarumin cigaba a fannin sadarwa, ta hanyar sauyi aka samu wajen yin hulda da jama’a.

Sauran wadanda suka gabatar da Makaloli kan matsalaolin da jami’an ke fuskanta, a yayin taron horaswar sun hadar da Dr. Ganiu Okunnu na Jami’ar jihar Legas (LASU) da Abayomi Adisa na BBC, sun bukaci mahalarta taron dasu yi amfani da kayan sadarwa na zamani a yayin da suke gudanar da ayyukan su.

Wanda suka ce yin hakan zai taimaka musu matuka wajen samun kyakkyawar alaka da wadanda suke son sakon ya isa gare su.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp