An Sami Bullar Kyandar Biri A Jihar Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta sanar da bullar cutar Kyandar biri karon farko a jihar, kuma sun masa magani sun sallame shi.

Kwamishinan lafiya na jihar Yakubu Danja, ne ya tabbatar da bullar cutar yayin da yake gabatar da fara rabon magungu kyauta a kananan hukumomi 34 dake fadin jihar.

Yace sun sami mutum 15 da ake zargin suna dauke da cutar kuma an dauki samfurin gwajin zuwa birnin tarayya Abuja, wanda yanzu haka ana sauraren sakamako.

Danja ya kuma bayyana cewa za’a raba magungunan kyauta ga cibiyoyin bada maganin a jihar, kana Gwamnatin ta himmatu wajen wayar da kan dukkan kungiyoyin bada Agajin gaggawa domin dakile yaduwar Cutar.

Ya kara da cewa daga cikin magungunan da aka raba domin dakile yaduwar cututtuka har da maganin cutar kwalara da sauran cutattukan dake da alaka da zuwan yanayin damuna.

Daga bisani kwamishinan ya zaga cibiyar bayar da Agajin gaggawa inda ya mika na’urar Firinji guda140 domin Ajje alluran, ya kuma tabbatar da cewa hukumar lafiya matakin farko ce ta bayar da su kyauta.

HealthDigest

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 7 minutes 51 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 49 minutes 16 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com