Home Labarai An Sami Bullar Kyandar Biri A Jihar Katsina

An Sami Bullar Kyandar Biri A Jihar Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta sanar da bullar cutar Kyandar biri karon farko a jihar, kuma sun masa magani sun sallame shi.

Kwamishinan lafiya na jihar Yakubu Danja, ne ya tabbatar da bullar cutar yayin da yake gabatar da fara rabon magungu kyauta a kananan hukumomi 34 dake fadin jihar.

Yace sun sami mutum 15 da ake zargin suna dauke da cutar kuma an dauki samfurin gwajin zuwa birnin tarayya Abuja, wanda yanzu haka ana sauraren sakamako.

Danja ya kuma bayyana cewa za’a raba magungunan kyauta ga cibiyoyin bada maganin a jihar, kana Gwamnatin ta himmatu wajen wayar da kan dukkan kungiyoyin bada Agajin gaggawa domin dakile yaduwar Cutar.

Ya kara da cewa daga cikin magungunan da aka raba domin dakile yaduwar cututtuka har da maganin cutar kwalara da sauran cutattukan dake da alaka da zuwan yanayin damuna.

Daga bisani kwamishinan ya zaga cibiyar bayar da Agajin gaggawa inda ya mika na’urar Firinji guda140 domin Ajje alluran, ya kuma tabbatar da cewa hukumar lafiya matakin farko ce ta bayar da su kyauta.

HealthDigest

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp