Home Labarai Rundunar Sojojin Ruwan Nijeriya ta Nemi Hadin Gwuiwar PRNigeria

Rundunar Sojojin Ruwan Nijeriya ta Nemi Hadin Gwuiwar PRNigeria

Babban hafsan sojin ruwa CNS, Vice Admiral Awwal Zubairu Gambo, ya bayyana farin cikinsa game da yadda PRNigeria ke wallafa labaran da ya shafi sojoji da fannin tsaro ba tare da nuna son rai ba.

Ya bayyana hakan ne ta bakin kakakin rundunar sojojin Ruwan Commodore Adetun Ayo-Vaughan, wanda ya jagoran tawagar jami’an rundunar wata ziyarar kafa da kafa zuwa hedikwatar jaridar dake Birnin tarayya Abuja.

A cewar, PRNigeria zata cigaba da kasancewa kamfanin dillancin labarai na daya kuma taka tabbatar da wallafa da sahihin labari kan ayyukan sojoji da sauran jami’an tsaro.

Yace: PRNigeria ta tabbatarwa da kanta tsayuwa kan gwadaben wallafa labaran gaskiya da gaskiya kan lamurran tsaro musamman sojojin Nijeriya.

Ya kara da cewa sojojin Nijeriya sun yaba da ayyukan PRNigeria. Don haka kakakin rundunar yace akwai bukatar a bunkasa alakar dake akwai tsakanin rundunar da Jaridar ta PRNigeria.

Da yake karbar bakin, babban Editan rukunin jaridun dake karkashin kamfanin Image Merchants Promotion (IMPR) Limited dake mallakin PRNigeria Mal. Yusha’u Shuaib, ya yaba kakakin rundunar sojin Ruwan bisa wannan ziyara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp