Home SIYASA Buhari ya Rantsar da Mai shari’a Ariwoola a Matsayin Babban CJN

Buhari ya Rantsar da Mai shari’a Ariwoola a Matsayin Babban CJN

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rantsar da Justice Olukayode Ariwoola a matsayin babban alkalin alkalan Najeriya (CJN).

Bikin rantsuwar da ya gudana gabanin fara taron majalisar zartarwa ta tarayya na mako, (FEC), ya samu halartar mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, da gwamnonin jihohin Oyo da Ondo, Seyi Makinde da Rotimi Akeredolu.

sai kuma Sauran alkalan kotun kolin Najeriya wadanda a matsayin wadanda suka halarci bikin; Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Boss Mustapha; Shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya, Dr Folasade Yemi-Esan; Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno (Rtd).

Sauran sun hadar da ministocin da suka shigo domin halartar taron majalisar na mako, ciki har da Hadi Sirika (Aviation); Olorunnimbe Mamora (Kimiyya, Fasaha); Chris Ngige (Kwadago da Nagartar Aiki); Abubakar Malami (Ministan shari’a, Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya); Niyi Adebayo (Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari); Babatunde Fashola (Ayyuka da Gidaje); Abubakar Aliyu (Makamashi) da sauransu.

Da yake zantawa da manema labarai bayan rantsar da shi, Mai shari’a Ariwoola ya yi kira ga ‘yan siyasa a kasar nan da su kyale bangaren shari’a ya yi aiki yadda ya kamata ganin yadda zaben 2023 ke gabatowa yayin da ya yi alkawarin kawo gyara a kotun koli.

A nasa bangaren, gwamna Seyi Makinde ya bayyana godiya a madadin jama’a da gwamnatin jihar Oyo ga shugaban.

A halin da ake ciki, majalisar ta yi shiru na minti daya domin karrama tsohon ministan ayyuka na musamman kuma shugaban jam’iyyar PDP, Cif Vincent Ogbulafor, wanda ya rasu kwanan nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp