Home Labarai Gwamnatin Jihar Zamfara ta Rufe wasu Yankuna a Jihar Saboda Tsaro

Gwamnatin Jihar Zamfara ta Rufe wasu Yankuna a Jihar Saboda Tsaro

Gwamnatin jihar Zamfara ta ce ta ɗauki matakin dakatar da kowace irin hada-hada a wasu yankunanta da ke fama da matsalar tsaro.

wannanna kunshe ne ta cikin wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar a ranar Juma’a, ta ce ta lura da yadda ake samun taɓarɓarewar tsaro ta hanyar sace-sacen al’umma a kauyuka da kuma kan wasu hanyoyin jihar.

A saboda haka sanarwar ta ce gwamnati ta kulle,  ƙananan hukumomin Anka da Bukuyum da kuma Gummi ɗungurungum.

Sauran kauyukan da kullewar ta shafa su ne Ƴarkofoji, da Birnin Tudu, da Rini, da Gora Namaye, da Janbako, da Faru, da Boko da kuma Mada.

Sanarwar ta kuma ce daga yau an rufe kasuwannin Danjibga da Bagega, Bugu da ƙari an dakatar da zirga-zirga kan hanyoyi da suka hadar da Colony zuwa Lambar Boko, Bakura zuwa Lambar Damri, Mayanchi zuwa Daki Takwas har zuwa Gummi, Daki Takwas zuwa Zuru, Kucheri zuwa Bawaganga zuwa Wanke, Magami zuwa Dangulbi sai kuma  Gusau zuwa Magami

Gwamnati ta ce an ɗauki matakin ne domin bai wa jami’an tsaro damar gudanar da ayyukansu ba tare da wani cikas ba.

Ta kuma ce ta bai wa jami’an tsaro umurnin ɗaukan mummunan mataki kan duk wanda aka samu da laifin karya dokar.

jihar Zamfara na  guda cikin jihohin  Arewa maso yammacin Nijeriya da matsalar tsaro kekara karama sakamakon  ƴanfashin daji da ta fi kassarar jihar dama yankin.

PRNigeria Haus

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp