Home Labarai UNICEF: Yara Sama da Dubu 14 na Cikin Hadarin Kamuwa da...

UNICEF: Yara Sama da Dubu 14 na Cikin Hadarin Kamuwa da Cutar Yunwa a Nijeriya

Asusun tallafawa kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya yi gargadin cewa kananan yara miliyan 14 da dubu 700 a Najeriya galibinsu ‘yan kasa da shekaru 5 da haihuwa na cikin hadarin kamuwa da cutar Tamowa wadda karancin abinci me gina jiki ke haddasawa.

Asusu na UNICEF ya bayyana cewa idan har ba a dauki matakan da suka kamata ba, a cikin shekarar dake shirinkarewa, yara miliyan 13 za su fuskanci cutar tamowa yayin da wasu miliyan 1 da dubu 700 kuma za su fuskanci matsananciyar cutar ta Tamowa galibi a yankin arewacin Najeriyar

Asusun na UNICEF ya ce abin takaici ne yadda alkaluma ke nuna mutuwar kananan yara 100 ‘yan kasa da shekaru 5 da haihuwa duk bayan sa’a daya a Najeriya, yayin da wasu yaran na daban miliyan 12 ke cikin halin matsanancin rashin abinci.

Shugabar sashen abinci mai gina jiki ta UNICEF a Najeriya Nemat Hajeebhoy, ta ce yara a Najeriya na halin tsananin bukatar abinci mai gina jiki lura da yanayin da kasar ke ciki na tabarbarewar tattalin arzki da ya sanya iyalai gaza samun isasshen abinci.

A cewar jami’ar matsaloli masu alaka da ambaliyar ruwa da ta lalata tarin amfanin gona a sassan Najeriya na shirin sake tsananta karuwar yaran da ke fama da wannan cuta ta rashin isasshen abinci mai gina jiki wato cutar yunwa ko kuma Tamowa.

Nemat Hejeebhoy ta ce za a fuskanci karuwar yara masu fama da matsalar cutar ta Tamowa a 2023 saboda karancin abinci da Najeriya za ta fuskanta mai alaka da sauyin yanayi.

UNICEF ta ce idan har gwamnatoci da sauran wadanda abin ya shafa basu dauki matakan da suka kamata ba, rayuwar kananan yaran masu fama da yunwa na cikin hadarin gaske, kari kan miliyoyin yaran da yanzu haka ke fama da cutar ta Tamowa.

UNICEF

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp