Home Labarai ‘Yan Bindiga Sun Sace Hakimi a Jihar Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Sace Hakimi a Jihar Zamfara

Rahotanni daga jihar Zamfara dake arewa maso yammacin Najeriya na bayyana cewa ‘Yan bindiga sun yi awon gaba da hakimin gundumar Kwangami a karamar hukumar Zurmi ta jihar tare da wasu mutane 6.

Majiyoyi daga yankin sun ce ‘yan bindigar sun shiga garin ne da manyan makamai a ranar Litinin, inda suka jefa al’ummar kauyen cikin rudani, kuma suka dauke basaraken, Alhaji Muhammad Galadima.

Sun kara da cewa ‘yan ta’addan sun bi wadannan mutane har gidajensu ne suka dauke su.

A waje daya kuma, ‘yan bindiga ssun sako mutane 6  da suka sace a kauyen Kazauda na karamar hukumar Gusau a jihar Zamfara bayan da aka biya Naira miliyan 4 a matsayin kudin fansa.

Kawo yanzu dai rundunar ‘yan sandan jihar ba tace ba komai kan wannan batu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp