Home Labarai ASUU Tace Bazata Sake Shiga Yajin Aiki ba

ASUU Tace Bazata Sake Shiga Yajin Aiki ba

Kungiyar Malaman jami’o’I Nijeriya (ASUU) ta kawo karshen taronta na kwamitin zartarwa na kasa (NEC) inda ta yanke matsayar ba zata sake shiga wani yajin aiki ba.

Sai dai kungiyar ta yi Allah-wadai da yunkurin gwamnatin tarayya na mayar da malaman jami’o’i kamar ma’aikatan wucin gadi ta hanyar biyansu Rabin albashin su.

A wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar Talata bayan kammala taron NEC, shugaban ASUU na kasa, Farfesa Emmanuel Osodeke, ya bayyana cewa malaman jami’o’in cikakakkun ma’aikata ne ba na wucin gadi ba.

Ya ce kungiyar ta dakatar da yajin aikin na watanni takwas a ranar 14 ga Oktoba, 2022 bisa bin umarnin kotun ma’aikata ta kasa da kuma la’akari da kokarin tsoma bakin ‘yan Najeriya masu kishin kasa, ciki har da Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Femi Gbajabiamila.

Osodeke ya kara da cewa matakin da kungiyar ta dauka alamu ne da suka nuna tsantsar biyayyar ta ga bangaren shari’a, da sauran cibiyoyi da ma’aikatun gwamnati a kodayaushe da suke kira ga kungiyar data sanya kishin kasa fiye da bukatun kansu.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp