Home Labarai DHQ zata bada Miliyan Biyar ga wanda ke da bayani kan yadda...

DHQ zata bada Miliyan Biyar ga wanda ke da bayani kan yadda za’a cafke ‘yan ta’adda

Shalkwatan Tsaron Najeriya ya wallafa sunaye tare da hotunan wasu kwamandojin ‘yan ta’addar da suka addabi arewa maso gabashi da kuma arewa maso yammaci da tsakiyar arewacin Najeriya.

Shalkawatan tsaron ta ce, zata bada tukuicin Naira miliyan 5 ga duk wani dan Najeriya da ke da bayanai kan yadda za a iya cafke ‘yan ta’addar.

wannan dai na wani bangare na daukar matakin ci gaba da aikin kakkabe mayakan dake tayar da kayar baya a yankunan. abin da ta bayyana mayin aikin daya rataya a wuyan ta maido da da zaman lafiya a yankunan.

Sunayen ‘yan ta’addar da ake nema ruwa a jallo kamar yadda darektan yada labaran shalkwatan tsaron Manjo Janar Jimmy Akpor ya fitar, sun hadar da:

SANI DANGOTE – daga kauyen  Dumbarum, Karamar Hukumar Zurmi ta jihar Zamfara.

BELLO TURJI GUDDA – daga kauyen Dakai, jihar Zamfara.

LEKO – daga kauyen Mozol, jihar Katsina.

DOGO NAHALI – daga kauyen ‘yar tsamiya, Karamar Hukumar  Kankara, jihar Katsina.

HALILU SUBUBU – daga kauyen Sububu a Karamar Hukumar Maradun, jihar Zamfara.

NAGONA –  daga Angwan Galadima da ke ISA a jihar S|okoto.

NASANDA – daga kauyen Kwashabawa, Karamar Hukumar Zurmi, jihar Zamfara.

ISIYA KWASHEN GARWA – daga kauyen Kamfanin Daudawa da ke Faskari a jihar Katsina.

ALI KACHALLA da aka fi sani da  ALI KAWAJE – daga kauyen Kuyambara a jihar Zamfara.

ABU RADDE – daga kauyen Varanda a Karamar Hukumar Batsari, jihar Katsina.

DAN-DA – daga kauyen Varanda a Karamar Hukumar Batsari, jihar Katsina.

SANI GURGU – daga kauyen Varanda a Karamar Hukumar Batsari, jihar Katsina.

UMARU DAN NIGERIA – daga kauyen Rafi da ke Mada a Gusau, jihar Zamfara.

NAGALA – daga Maru a jihar Zamfara.

ALHAJI ADO ALIERO – daga kauyen Yankuzo, a Karamar Hukumar Tsafe, jiharZamfara.

MONORE – daga ‘Yantumaki, jihar Katsina.

GWASKA DANKARAMI – daga kauyen Shamushele a Karamar Hukumar Zuri, jihar Zamfara.

BALERI – daga Karamr Hukumar Shinkafi, jihar Zamfara.

MAMUDU TAINANGE – daga kauyen baranda, Karamar Hukumar Batsari, jihar Katsina.

daga bisani shalkwatar ta ce ga dukkan mai wani karin bayani kan wadannan ‘yan ta’adda sai ya kira 09135904467 domin yin bayani.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp