Home Labarai DHQ zata bada Miliyan Biyar ga wanda ke da bayani kan yadda...

DHQ zata bada Miliyan Biyar ga wanda ke da bayani kan yadda za’a cafke ‘yan ta’adda

Shalkwatan Tsaron Najeriya ya wallafa sunaye tare da hotunan wasu kwamandojin ‘yan ta’addar da suka addabi arewa maso gabashi da kuma arewa maso yammaci da tsakiyar arewacin Najeriya.

Shalkawatan tsaron ta ce, zata bada tukuicin Naira miliyan 5 ga duk wani dan Najeriya da ke da bayanai kan yadda za a iya cafke ‘yan ta’addar.

wannan dai na wani bangare na daukar matakin ci gaba da aikin kakkabe mayakan dake tayar da kayar baya a yankunan. abin da ta bayyana mayin aikin daya rataya a wuyan ta maido da da zaman lafiya a yankunan.

Sunayen ‘yan ta’addar da ake nema ruwa a jallo kamar yadda darektan yada labaran shalkwatan tsaron Manjo Janar Jimmy Akpor ya fitar, sun hadar da:

SANI DANGOTE – daga kauyen  Dumbarum, Karamar Hukumar Zurmi ta jihar Zamfara.

BELLO TURJI GUDDA – daga kauyen Dakai, jihar Zamfara.

LEKO – daga kauyen Mozol, jihar Katsina.

DOGO NAHALI – daga kauyen ‘yar tsamiya, Karamar Hukumar  Kankara, jihar Katsina.

HALILU SUBUBU – daga kauyen Sububu a Karamar Hukumar Maradun, jihar Zamfara.

NAGONA –  daga Angwan Galadima da ke ISA a jihar S|okoto.

NASANDA – daga kauyen Kwashabawa, Karamar Hukumar Zurmi, jihar Zamfara.

ISIYA KWASHEN GARWA – daga kauyen Kamfanin Daudawa da ke Faskari a jihar Katsina.

ALI KACHALLA da aka fi sani da  ALI KAWAJE – daga kauyen Kuyambara a jihar Zamfara.

ABU RADDE – daga kauyen Varanda a Karamar Hukumar Batsari, jihar Katsina.

DAN-DA – daga kauyen Varanda a Karamar Hukumar Batsari, jihar Katsina.

SANI GURGU – daga kauyen Varanda a Karamar Hukumar Batsari, jihar Katsina.

UMARU DAN NIGERIA – daga kauyen Rafi da ke Mada a Gusau, jihar Zamfara.

NAGALA – daga Maru a jihar Zamfara.

ALHAJI ADO ALIERO – daga kauyen Yankuzo, a Karamar Hukumar Tsafe, jiharZamfara.

MONORE – daga ‘Yantumaki, jihar Katsina.

GWASKA DANKARAMI – daga kauyen Shamushele a Karamar Hukumar Zuri, jihar Zamfara.

BALERI – daga Karamr Hukumar Shinkafi, jihar Zamfara.

MAMUDU TAINANGE – daga kauyen baranda, Karamar Hukumar Batsari, jihar Katsina.

daga bisani shalkwatar ta ce ga dukkan mai wani karin bayani kan wadannan ‘yan ta’adda sai ya kira 09135904467 domin yin bayani.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp