Home Labarai Ghana ta Gargadi ‘yan kasarta kan zuwa Nijeriya

Ghana ta Gargadi ‘yan kasarta kan zuwa Nijeriya

Gwamnatin Ghana ta gargadi ‘yan kasarta kan balaguro zuwa babban birnin tarayyar Najeriya Abuja saboda matsalar tsaro.

Wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar ranar Laraba ta ce gargadin ya biyo bayan mawuyacin hali da ake ciki a babban birnin kasar da kuma umarnin da hukumomi Najeriya suka bayar na a rufe otal-otal da ke gidajen kwana.

Sanarwar ta ta bukaci ‘yan kasar Ghana da dole sai sun shiga birnin Abuja da su tabbaatar sun dauki matakin kariya da taka tsan-tsan, inda ma’aikatar za ta ci gaba da sanya ido kan yadda al’umara ke ganuna tare da bayar da bayanai ga jama’a idan lamarin ya daidaita.”

Ana yawan tafiye-tafiye tsakanin Ghana da Najeriya, manyan kasashe biyu mafi karfin tattalin arziki a yammacin Afirka.

Hakan na zuwa ne makonni bayan Amurka da wasu ofisoshin jakadancin kasashen waje sun yi gargadi game da tafiye-tafiye zuwa babban birnin Najeriya saboda barazanar ta’addanci.

Sai dai gwamnatin Najeriya ta roki ‘yan kasar da su kwantar da hankulansu tana mai tabbatar musu da cewa jami’an tsaro na kokarin dakile duk wata barazanar ta’addanci.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp