Home Labarai INEC za ta Tattauna da Ganduje, Bala Muhammad, da Jami’an Tsaro Kan...

INEC za ta Tattauna da Ganduje, Bala Muhammad, da Jami’an Tsaro Kan Batutuwan Zaben 2023

Hukumar zabe mai zaman kanta za ta tattauna da jiga-jigan siyasar kasar nan kan batutuwan da suka shafi zaben 2023.

An gayyaci wasu gwamnoni, dan takarar shugaban kasa da sauran masu ruwa da tsaki na kasar nan.

Majiya ta bayyana maudu’in da za a tattauna a kai don shawo kalubalen tsaro a zaben 2023 mai zuwa na badi.

FCT, Abuja – Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) a ranar Talata mai zuwa za ta gana da gwamnoni, jami’an tsaro da dan takarar shugaban kasa gabanin zaben 2023 mai zuwa nan kusa.

Za a yi tattaunawar ne a Nicon Luxury a birnin tarayya Abuja tare da kwamishinan INEC kan harkokin wayar da masu kada kuri’u, Festu Okoye, Punch ta ruwaito.

A bangaren ‘yan siyasa, za a zauna da gwamna Abdullahi Ganduje na Kano, gwamna Bala Muhammad na Bauchi da gwamna Samuel Ortom na jhar Benue.

A bangaren hukumomin tsaro, za a yi zaman tare da sufeta janar na ‘yan sanda, Usman Alkali Baba da dai sauransu.

Hakazalika, za a yi da dan takarar shugaban kas ana jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, shugaban majalisar zauren shawarin jam’iyyun siyasa, Yabagi Sani, kungiyar ‘yan jarida da sauran masu ruwa da tsaki a harkar zabe.

Wannan batu dai na fitowa ne a cikin wata sanarwa da wanda ya shirya zaman, Edwin Olofu ya fitar a ranar Laraba 16 ga watan Nuwamba.

Olofu, wanda kuma shine manajan daraktan jarida Platinum Post ya bayyana cewa, wadanda za su halarci zaman za su tafka muhawara ne kan yadda za a yi zabe cikin lumana a badi.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, Hamza Al-Mustapha zai yi fashin baki kan maudu’i matsalolin na zamani da kalubalensu da kuma illar hakan ga zaben 2023.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp