Home Labarai ‘Yan Majalisa a Jihar Ekiti Sun Tsige kakakin Majalisar

‘Yan Majalisa a Jihar Ekiti Sun Tsige kakakin Majalisar

‘Yan majalisa 17 cikin jerin 25 da ake da su a zauren majalisar dokokin jihar Ekiti dake kudancin Najeriya sun zabi Olubunmi Adelugba a matsayin sabon kakakin majalisar dokokin jihar.
Wannan dai ya biyo bayan dakatarwar da majalisar ta yiwa tsohon kakakin majalisar dokokin Rt. Hon. Gboyega Aribisogan da kuma kuri’ar da suka kada na tsige shi daga kan mukaminsa daga bisani.
Idan dai za a iya tunawa majalisar dokokin jihar Ekiti ta tsinci kanta a cikin yanayi na rikice-rikice tun bayan da Hon Funminiyi Afuye dake zama kakakin majalisar dokokin ya rasu a ranat 19 ga watab Oktoban da ya gabata.
Rikicin da a baya ya yi sanadiyyar kulle majalisar dokokin jihar bayan da aka samu rabuwar kawuna a tsakanin mambobin majalisar inda wani tsagi ya goyi bayan jam’iyyar dake adawa a jihar

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp