Home General Burtaniya ta Gargadi ‘Yan Siyasar Nijeriya

Burtaniya ta Gargadi ‘Yan Siyasar Nijeriya

Gwamnatin Birtaniya ta sake gargadin ‘yan siyasar Najeriya da ke tunzira magoya bayansu wajen tada hankali ko kuma rikicin da ke kai ga rasa rayuka da su kwan da sanin cewar ba za ta ba su izinin shiga kasarta ba.

Wannan na zuwa ne gabatowar babban zaben kasar, wanda wasu cikin ‘yan siyasar ke amfani da damar wajen tada tarzoma lura da yadda irin wadannan matsaloli ke yi wa shirin zaben shekarar 2023 barazana.

Babbar Jami’ar Diflomaisyar kasar Catriona Lang ta bayyana haka lokacin da ta jagoranci tawagar manyan jami’anta domin ganawa da shugabannin ‘yan kwamitin zartarwar jam’iyyar adawa ta PDP.

Lang ta ce zaben shekarar 2023 na da matukar muhimmanci ga Afirka da kuma duniya baki daya, saboda haka hankalin Birtaniya da kuma kasashen duniya ya karkata akan kasar.

Jami’ar ta ce Birtaniya ta yi matukar damuwa da irin laifuffukan da ke da nasaba da zabe 52 da aka gani a jihohi daban-daban har 22, ciki har da harin da aka kai wa tawagar jam’iyyar PDP a Jihar Borno.

Lang ta ce suna cike da damuwa akan irin wadannan tashe-tashen hankula, saboda haka suka bukaci tattaunawa da shugabannin jam’iyyar akan irin matakan da suka dace a dauka domin tabbatar da ganin an yi zaben cikin kwanciyar hankali.

Birtaniya ta ce yana da wahala mutane su fito su yi zabe muddin suna fuskantar takala ko barazana, yayin da wadannan abubuwa na iya shafar kimar zaben baki daya.

Lang ta ce za su ci gaba da sanya ido akan ‘yan siyasar da ke tada hankali ko kuma tinzira jama’a tada hankalin wajen amfani da kafofin yada labarai daga kowacce jama’iyya domin daukar mataki akansu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp