Home Labarai Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Hallaka Mayakan ISWAP 24

Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Hallaka Mayakan ISWAP 24

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami nasarar hallaka mayakan ISWAP dake tsaka da karbar horo da IED ta samar a yankin tafkin Chadi.

Wani harin sama da dakarun sojojin saman Nijeriya suka kai kan mayakan kungiyar boko haram tsagin ISWAP yayi sanadiyyar mutuwar mayakan 24.

PRNigeria ta ruwaito cewa atisayen ya faru ne ranar lahadi a Tumbum hamma, guda cikin sananne wurin da mayakan na ISWAP ke karbar hro a yankin Tafkin Chadi.

Wata majiyar liken asiri ta tsaro ta shaidawa PRNigeria cewa ‘yan ta’addan da aka hallaka na gudanar da aikin sarrafa makami da kuma hada bama-bamai wadanda ke karbar horo har tsawon kwanaki shida (6) a jere.

A wani labarin makamancin wannan, PRNigeria ta tattaro cewa wani jirgin yakin sojojin saman Nijeriya (NAF) karkashin rundunar sojin sama ta Operation Hadin kai (OPHK) ya kai wasu hare-hare ta sama kan wata maboyar ‘yan ta’adda a Tumbun da ke kusa da tafkin Chadi.

Wannan wani bangare ne na martani kan mayakan bisa yunkurin sun a kai hari wani sansanin soojin Nijeriya da ke Mallam fatori.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp