Home Labarai Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Hallaka Mayakan ISWAP 24

Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Hallaka Mayakan ISWAP 24

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami nasarar hallaka mayakan ISWAP dake tsaka da karbar horo da IED ta samar a yankin tafkin Chadi.

Wani harin sama da dakarun sojojin saman Nijeriya suka kai kan mayakan kungiyar boko haram tsagin ISWAP yayi sanadiyyar mutuwar mayakan 24.

PRNigeria ta ruwaito cewa atisayen ya faru ne ranar lahadi a Tumbum hamma, guda cikin sananne wurin da mayakan na ISWAP ke karbar hro a yankin Tafkin Chadi.

Wata majiyar liken asiri ta tsaro ta shaidawa PRNigeria cewa ‘yan ta’addan da aka hallaka na gudanar da aikin sarrafa makami da kuma hada bama-bamai wadanda ke karbar horo har tsawon kwanaki shida (6) a jere.

A wani labarin makamancin wannan, PRNigeria ta tattaro cewa wani jirgin yakin sojojin saman Nijeriya (NAF) karkashin rundunar sojin sama ta Operation Hadin kai (OPHK) ya kai wasu hare-hare ta sama kan wata maboyar ‘yan ta’adda a Tumbun da ke kusa da tafkin Chadi.

Wannan wani bangare ne na martani kan mayakan bisa yunkurin sun a kai hari wani sansanin soojin Nijeriya da ke Mallam fatori.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp