Home General Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara ta kubutar da Tsoho dan Shekara 75...

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara ta kubutar da Tsoho dan Shekara 75 daga hannun ‘Yan Ta’adda

Rundunar ‘yan sanda jihar zamfara ta sami nasarar kubutar da wani tsoho mai kimanin shekaru 75 daga hannun ‘yan Ta’adda a jihar.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin rundunar SP Mohammed Shehu Anipr, a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar CP Kolo Yusuf psc.
Sanarwar tace rundunar a ranar Juma’a ta sami nasarar kubutar da tsohon mai suna Muhammad Shehi dan asalin garin Enagi a karamar hukumar Edati ta jihar Niger, bayan ya kwashe watanni a hannun ‘yan bindigar.
Dakarun rundunar sun gudanar da atisayen ne bayan samun wani rahoton sirri kan sace tsohon, nan suka shiga aiki ba dare ba rana har sai da suka sami nasarar kubutar da shi.
Tsohon ya bayyana wa jami’an cewa wasu gungun ‘yan ta’adda da suka tare hanyar birnin Gwari zuwa Kaduna a farkon watan Oktoban 2022, suka yi awon gaba da su zuwa cikin daji a wani yanki na dan sadau dake jihar ta Zamfara, inda ya kwashe watanni 2 a hannun su.
Sanarwa tace Likitocin sun gudanar da binciken lafiyar sa kafin Jami’an ‘yan sandan su sadashi da iyalen sa.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar ya taya ‘yan uwa da iyalen Muhammad murna bisa samun dan uwan su da suka yi daga bisani ya tabbatar da kudirin hukumar na kare lafiya da dokiyoyin Al’umma

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp