Home General Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara ta kubutar da Tsoho dan Shekara 75...

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara ta kubutar da Tsoho dan Shekara 75 daga hannun ‘Yan Ta’adda

Rundunar ‘yan sanda jihar zamfara ta sami nasarar kubutar da wani tsoho mai kimanin shekaru 75 daga hannun ‘yan Ta’adda a jihar.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin rundunar SP Mohammed Shehu Anipr, a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar CP Kolo Yusuf psc.
Sanarwar tace rundunar a ranar Juma’a ta sami nasarar kubutar da tsohon mai suna Muhammad Shehi dan asalin garin Enagi a karamar hukumar Edati ta jihar Niger, bayan ya kwashe watanni a hannun ‘yan bindigar.
Dakarun rundunar sun gudanar da atisayen ne bayan samun wani rahoton sirri kan sace tsohon, nan suka shiga aiki ba dare ba rana har sai da suka sami nasarar kubutar da shi.
Tsohon ya bayyana wa jami’an cewa wasu gungun ‘yan ta’adda da suka tare hanyar birnin Gwari zuwa Kaduna a farkon watan Oktoban 2022, suka yi awon gaba da su zuwa cikin daji a wani yanki na dan sadau dake jihar ta Zamfara, inda ya kwashe watanni 2 a hannun su.
Sanarwa tace Likitocin sun gudanar da binciken lafiyar sa kafin Jami’an ‘yan sandan su sadashi da iyalen sa.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar ya taya ‘yan uwa da iyalen Muhammad murna bisa samun dan uwan su da suka yi daga bisani ya tabbatar da kudirin hukumar na kare lafiya da dokiyoyin Al’umma

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp